Wani jirgi mara matuki da ya tarwatse ya lalata wani katafaren ginin a birnin Abu Dhabi dake kusa da ofishin jakadancin Isra’ila da wasu ofisoshin jakadanci na kasa da kasa da dama, lamarin da ya haddasa kananan raunuka ga wata mata da yaronta, kamar yadda ofishin yada labarai na gwamnatin Abu Dhabi ya sanar da yammacin ranar Lahadi.
tarkacen jirgin mara matuki sun fado a gaban wani ginin Etihad Towers, bayan wata na’ura ta hana makamin fashewa a kasa, in ji ofishin yada labaran.
Bayan da Amurka da Isra’ila suka kaddamar da hare-hare kan Iran a ranar Asabar, Iran ta ce za ta kai hari kan sansanonin Amurka da ke yankin. Amma kuma ta afkawa yankuna da dama na farar hula da na kasuwanci a duk fadin garuruwan yankin Gulf, lamarin da ke kara fadada tasirin rikicin kan muhimman cibiyoyin zirga-zirgar jiragen sama da na kasuwanci a yankin.
Yayin da hare-haren ramuwar gayya ke ci gaba da yaduwa a jiya Lahadin, sun sake yin kaca-kaca a sassan kasashen Larabawa na yankin Gulf, inda aka ji karar fashewar abubuwa masu karfi a Dubai da Doha babban birnin Qatar da kuma Oman a karon farko.
Sanarwar da ofishin yada labaran gwamnatin Dubai data fitar ta ce, a birnin Dubai, wasu mutane biyu sun jikkata bayan da wasu tarkacen jiragen sama marasa matuka suka fado kan gidaje biyu lokacin da aka kama su.


