Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Yunkurin Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi Na Kara Kankama A Najeriya
Published: March 13, 2026 at 8:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Yunkurin samadda ‘yan sandan jihohi na kara kankama a Najeriya, tun bayan da sufeta janar na ‘yan sandan Najeriya, Olatunji Disu ya kaddamar da wani komiti mai mutane takwas da zai duba yadda za’a aiwatar da ‘yan sandan jihohi a Najeriya.

Sufetan janar na ‘yan sandan wanda ya jaddada cewa babu gudu babu ja da baya kan yin garambawul da samadda ‘yan sanda jihohi, ya kuma ce ayyukan ‘yan sandan jihohin ba zai gurgunta ayyukan ‘yan sandan Najeriya ba.

Kan haka ne, Gwamnan jahar Filato, Caleb Mutfwang shima ya kaddamar da komiti mai mutane goma sha hudu da zasu bada shawarwari kan kafa rundunar ‘yan sandan jiha don karfafa tsaro a Jihar Filato.

Gwamnan yace komitin zai yi nazari kan batun samadda ‘yan sanda a jihar bisa tsarin gwamnatin tarayya da bada shawarwari da zasu taimaka a tattaunawar da ake yi a kasa kan sauye-sauye da ake yi na samadda tsaro.

Honarabul Musa Yunusa Ayiga, tsohon mataimakin shugaban kungiyar kwadago bangaren masu samarda wutar lantarki a Najeriya yace baiwa gwamnoni damar kafa ‘yan sandan jihohi bai dace ba.

A bangare guda kuwa, Rabaran Ayuba Asheshe yace suna addu’ar Allah ya tabbatar da alheri.

Sufeta janar na ‘yan sandan Najeriya, Olatunji Disu yace kiraye-kirayen da suke samu na karfafa hanyoyin tsaro a cikin kasar, shine ya sanya su daukan matakin kaddamar da komitin da ya bashi wata guda ya gabatar da rahotonsa.

Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana a jihar Filato Zainab Babaji ta aiko mana rahoto

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/AUD-20260313-WA0041.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya
Next Post: Shugaban Amurka Donald Trump Yace Amurka Zata Kai Babban Farmaki Iran

Karin Labarai Masu Alaka

Isra’ila Zata Mamaye Lebanon Labarai
Hanyar Gombe Dukku Darazo Ta Zamo Abun Damuwa Ga Al’ummar Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
Sojojin Amurka Sunfara Isowa Gabas Ta Tsakiya Amurka
Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Afrika
Gwamnatin Tarayyar Najeriya Zata Raba Taki Ga Manoma Afrika
Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamna Fubara: Rashin Kariya daga PDP Ne Ya Tilasta Ni Komawa APC Siyasa
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
  • Hukumar EFCC Ta Kama Dan Kasuwa A Kamaru Afrika
  • Hamas Ta Kwance Damara Afrika
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal Afrika
  • Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.