Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Yunkurin Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi Na Kara Kankama A Najeriya
Published: March 13, 2026 at 8:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Yunkurin samadda ‘yan sandan jihohi na kara kankama a Najeriya, tun bayan da sufeta janar na ‘yan sandan Najeriya, Olatunji Disu ya kaddamar da wani komiti mai mutane takwas da zai duba yadda za’a aiwatar da ‘yan sandan jihohi a Najeriya.

Sufetan janar na ‘yan sandan wanda ya jaddada cewa babu gudu babu ja da baya kan yin garambawul da samadda ‘yan sanda jihohi, ya kuma ce ayyukan ‘yan sandan jihohin ba zai gurgunta ayyukan ‘yan sandan Najeriya ba.

Kan haka ne, Gwamnan jahar Filato, Caleb Mutfwang shima ya kaddamar da komiti mai mutane goma sha hudu da zasu bada shawarwari kan kafa rundunar ‘yan sandan jiha don karfafa tsaro a Jihar Filato.

Gwamnan yace komitin zai yi nazari kan batun samadda ‘yan sanda a jihar bisa tsarin gwamnatin tarayya da bada shawarwari da zasu taimaka a tattaunawar da ake yi a kasa kan sauye-sauye da ake yi na samadda tsaro.

Honarabul Musa Yunusa Ayiga, tsohon mataimakin shugaban kungiyar kwadago bangaren masu samarda wutar lantarki a Najeriya yace baiwa gwamnoni damar kafa ‘yan sandan jihohi bai dace ba.

A bangare guda kuwa, Rabaran Ayuba Asheshe yace suna addu’ar Allah ya tabbatar da alheri.

Sufeta janar na ‘yan sandan Najeriya, Olatunji Disu yace kiraye-kirayen da suke samu na karfafa hanyoyin tsaro a cikin kasar, shine ya sanya su daukan matakin kaddamar da komitin da ya bashi wata guda ya gabatar da rahotonsa.

Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana a jihar Filato Zainab Babaji ta aiko mana rahoto

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/AUD-20260313-WA0041.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya
Next Post: Shugaban Amurka Donald Trump Yace Amurka Zata Kai Babban Farmaki Iran

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci Afrika
Shugaba Trump Ya Kara Matsin Lamba Kan Iran Amurka
An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami Afrika
Harin Jirgi Maras Matuki Ya Hallaka Mutane A Sudan Labarai
Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
Hukumar Zaben Najeriya Ta Sanar Da Ranar Zaben Shugaban Kasa Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Nnamdi Kanu Zai Daukaka Kara Har Zuwa Kotun Koli Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka. Najeriya
  • Barcelona Ta Lashe Kofin Spanish Super Cup  Wasanni
  • Emmanuel Macron: Yakamata Wani Sashi Ya Rika Takawa Wani Sashi Birki A Tsarin Demokradiya Amurka Amurka
  • Masarautar Borgu a Jihar Neja na neman daukin Gwamnatin Najeriya akan matsalar rashin tsaro Najeriya
  • Jirgin Sama Ya Fadi A Kano Labarai
  • Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora Wasanni
  • Shugaban Kasar Iran Yace Kasar Bata Da Kiyayya Tsakaninta Da Amurkawa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.