Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya
Published: November 25, 2025 at 8:38 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 25, 2025

Hukumar abinci ta Majalisar Dinkin Duniya (MDD) ta ce hare-haren ‘yan bindiga a yankin Arewacin Najeriya zai haddasa bala’in rashin abinci da ya fi na ko’ina muni a Nahiyar Afirka a cikin shekara mai zuwa.

A wani rahoton da hukumar ta wallafa yau Talata, ta yi kiyasin cewa mutane kimanin miliyan 35 zasu iya fuskantar yunwa a Najeriya a shekara mai zuwa, wanda zai kasance shine mafi muni a duk fadin nahiyar Afirka, kuma mafi muni da za a gani a cikin Najeriya tun daga lokacin da hukumar ta fara tattara irin wadannan alkaluma.

Hukumar ta kuma ce akwai mutane kimanin dubu 15 da zasu fuskanci bala’in mummunar yunwa mai iya kaiwa ga hallaka a Jihar Borno a shekara mai zuwa. Hukumar zata dora jihar Borno a mataki na 5 na bala’in yunwa, wanda shine matakin mafi muni na rashin abinci, kamar irin yadda ake gani a Gaza da Sudan.

Hukumar, wadda ake kira WFP a takaice, ta ce yankin Arewacin Najeeriya zai fuskanci bala’in yunwa mafi muni da bai taba gani ba cikin shekaru 10, inda manoma da mazauna karkara zasu fi shan wahala.

Jami’ain suka ce hare-haren ‘yan bindiga dabam dabam sun hana manoma yin amfani da gonakinsu a Arewa, yayin da a watan Oktoba aka samu wata sabuwar kungiyar ‘yan ta’addar da ita ma ta shiga cikin Najeriya. Wannan kungiya mai suna Jama’at Nusrat al-Islam wal Muslimin, ta saba kai hare-hare a yankin bakin iyakar Nijar, Mali da Burkina Faso.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi
Next Post: Gangamin Wayar Da Kai Don Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Jihar Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Rasha Takai Mummunan Hari Birnin Kyiv Afrika
Gwamnatin Kano Ta Rufe Gidajen Bukukuwa Da Shakatawa Labarai
Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata Labarai
Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya
Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya Afrika
Hukumomin Tsaron Najeriya Ne Suka Bukaci Amurka Ta Turo Musu Sojoji Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya Labarai
  • Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai
  • Dangote Ya Rage Farashin Mai A Najeriya Labarai
  • Akwai Yiwuwar Shugaban Ƙasar Afirka Ta Tsakiya Touadera Yasamu Nasara A Karo Na Uku Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.