Dangantakar Iran da kasashen yankin Gulf, za ta bukaci yin nazari mai zurfi dangane da yakin da Amurka da Isra’ila ke yi kan Iran, tare da takaita karfin ikon kasashen ta yadda yankin zai samu ci gaba, in ji jakadan Tehran a Saudiyya jiya Lahadin.
Ambasada Alireza Enayati da aka tambaye shi ko ya damu da cewa yakin zai yi illa ga dangantaka, ya ce, “Tambaya ce mai inganci, kuma amsar na iya zama mai sauki. Mu makwabta ne kuma ba za mu iya yi ba tare da juna ba; za mu bukaci yin nazari sosai.”
“Abin da yankin ya gani a cikin shekaru 50 da suka gabata, shi ne sakamakon wani tsari na kebancewa a yankin da kuma dogaro da wuce gona da iri kan ikon waje,” in ji shi a rubutacciyar amsa ga tambayoyi, yana mai kira da a zurfafa dangantaka tsakanin mambobi shida na kwamitin haɗin gwiwar yankin Gulf, tare da Iraki da Iran.
Kasashen Larabawa na yankin Gulf sun fuskanci hare-haren makami mai linzami da jirage sama da 2,000 tun bayan barkewar yakin a ranar 28 ga watan Fabrairu, tare da hare-haren da suka hada da ofisoshin diflomasiyya na Amurka da sansanonin soji har ma da muhimman ababen more rayuwa na man fetur na yankin Gulf, tashoshin jiragen ruwa, filayen jiragen sama, otal da gine-gine da gidaje.


