Ukraine da Syria sun yi alƙawarin ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro a tattaunawar da suka gudanar a jiya Lahadi, kamar yadda shugaban Ukraine, Volodymyr Zelenskyy, ya bayyana, yayin da Kyiv ke ƙoƙarin faɗaɗa ƙwarewar ta a fannin soja a yankin, bayan barkewar yaƙin Amurka, Isra’ila da Iran.
Zelenskyy, wanda ke ci gaba da rangadin ƙasashen Gabas ta Tsakiya, ya gana da takwaransa na Syria, Ahmed al-Sharaa, a babban birnin ƙasar, Damascus.
“Mun amince za mu yi aiki tare domin samar da ƙarin tsaro da damar ci gaba ga al’ummominmu,” in ji Zelenskyy a cikin wani saƙo da ya wallafa a dandalin Telegram.
A wani saƙo na gaba, Zelenskyy ya ce sun yi tattaunawa mai faɗi da shugaban Syria, tare da wani taron tattaunawa na ɓangarori uku da ya haɗa da ministan harkokin wajen Turkiyya, Hakan Fidan.
“Mun tattauna komai: daga batutuwan tsaro da kariya, da halin da yankin ke ciki sakamakon abubuwan da ke faruwa dangane da Iran, har zuwa haɗin gwiwa a fannin makamashi da gina ababen more rayuwa tsakanin ƙasashenmu,” in ji Zelenskyy.


