Wata kotu a babban birnin tarayyar Najeriya Abuja ta kama fiye da mutane 300 da alifin ta’addanci a ranar Jumu’a, a wani zaman kotu da aka shafe kwanaki hudu ana yi.
An fara zaman sauraren karar a kotu ne ranar Talata, inda yawanci wadanda aka gurfanar suka amsa laifin da gwamnatin Najeriya ke tuhumar su da shi.
Da yawa daga cikin su tuni an yanke musu hukuncin zaman shekaru 20 a gidan kurkuku, bayan da suka gurfana gaban alkalai goma.


