Aƙalla mutane goma sha ɗaya sun rasa rayukansu bayan ‘yan bindiga sun kai harin ramuwar gayya a wasu ƙauyuka da ke Ƙaramar Hukumar Kankia a jihar Katsina Najeriya
Majiyoyi rawaito cewa rundunar ƴan sandan jihar ta bayyana cewa harin ya faru ne da misalin ƙarfe 12 na rana a jiya Lahadi, inda maharan suka sake taruwa suka kai farmaki ƙauyukan Jeka da Kolo da Kwalgoro, suka buɗe wuta kan mazauna yankin, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutum 11 kafin jami’an tsaro su fatattake su.
Kwamishinan yan sandan jihar, CP Ali Umar Fagge, ya yi Allah-wadai da harin, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasu. Ya kuma ba da umarnin a ƙaddamar da farautar masu laifin ta hanyar amfani da bayanan sirri domin cafke su.
Mai magana da yawun rundunar, DSP Abubakar Sadiq, ya ce an ƙara yawan sintiri da aikin share dazuka domin gano maharan da suka tsere, tare da hana aukuwar irin wannan hari a gaba.
Rundunar ta kuma buƙaci al’umma da su kasance masu lura tare da bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro.
A cewar ‘yan sanda, harin ramuwar gayyar ya biyo bayan nasarorin da jami’an tsaro suka samu a baya-bayan nan, ciki har da dakile satar shanu da kuma kwato dabbobi sama da 200, da kuma fatattakar wasu ‘yan bindiga a wani hari da suka kai.
Hakazalika, gwamnatin jihar Katsina ta yi tir da harin, tana mai cewa hari kan fararen hula aiki ne na ta’addanci. Ta kuma jaddada aniyar ci gaba da haɗin gwiwa tsakanin al’umma da jami’an tsaro domin magance matsalar tsaro.


