Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Yara Miliyan 16 Sun Amfana Da Azithromycin A Karkashin Shirin SARMAAN Afrika

Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko
Published: September 10, 2026 at 6:00 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ma’aikatan Babban Bankin Najeriya (CBN), reshen Gombe, sun gyara Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin farko da ke Wajari, a Ƙaramar Hukumar Yamaltu Deba ta jihar Gombe, a matsayin wani ɓangare na shirin tallafa wa al’umma na kamfanin, wato CSR.

A cewar wata sanarwa da Jami’in Yaɗa Labarai na Ƙaramar Hukumar Yamaltu Deba, Comrade Babangida Umar Deba, ya sanya wa hannu, an ƙaddamar da cibiyar kiwon lafiyar da aka gyara a wani biki da ya samu halartar shugabannin al’umma, wakilan gwamnati da jami’an Babban Bankin Najeriya..

Da yake jawabi a wajen bikin, Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Yamaltu-Deba, Alhaji Mohammed D. Jalo, wanda ya wakilci Shugaban Ƙaramar Hukumar, Alhaji Yunusa Yakubu, ya yaba wa ma’aikatan CBN bisa zaɓar Wajari domin aiwatar da wannan aikin.

Ya bayyana wannan mataki a matsayin wata alama ta tausayi da kuma ƙudurin inganta jin daɗi da walwalar al’ummomin da ke karɓar ayyukan ma’aikatan, tare da gode musu da addu’ar Allah Ya saka musu da alheri.

Shi ma ɗan majalisar dokokin jihar Gombe mai wakiltar mazabar Deba, Alhaji Mohammed Kabiru Kuri, ya yi kira ga al’ummar Wajari da su ɗauki cibiyar a matsayin tasu, tare da tabbatar da cewa an kula da ita yadda ya kamata domin amfanin al’ummar yanzu da kuma na ƙarni masu zuwa.

A nasa jawabin, Hakimin Wajari kuma Wamban Deba, ya bayyana godiya ga ma’aikatan CBN bisa wannan tallafi, yana mai cewa gyaran cibiyar babbar gudummawa ce ga lafiyar al’umma da jin daɗinsu.

Ya kuma yi kira da a ƙara kai irin waɗannan ayyukan ci gaba zuwa Wajari da sauran al’ummomin da ke makwabtaka da yankin.

A wata Tattaunawa da Kansilan Gundumar Wajari, Malam Musa Hassan Wajari, ya ce an lalata tare da wawushe cibiyar kiwon lafiyar tsawon shekaru, ba tare da samun kulawar da ta dace ba, duk da kai rahotanni ga hukumomin da abin ya shafa.

Ya ce shiga tsakani da ma’aikatan CBN suka yi ne ya taimaka wajen dawo da cibiyar cikin yanayin da za ta iya ci gaba da gudanar da ayyukanta, inda ya buƙaci mazauna yankin su sanya ido tare da kare cibiyar daga sake fuskantar ɓarna.

Da yake magana kan wannan shiri, Shugaban Reshen CBN na Gombe, Alhaji Yunusa Buba Mubi, ya bayyana cewa gyaran cibiyar na daga cikin al’adun ma’aikatan CBN na bayar da gudummawa daga cikin abin da suke samu domin tallafa wa al’ummomin da suke gudanar da ayyukansu a cikinsu.

A cewarsa, wannan mataki wata hanya ce ta nuna godiya ga al’ummomin da ke samar da zaman lafiya da yanayi mai kyau da ke ba ma’aikatan CBN damar gudanar da ayyukansu cikin kwanciyar hankali.

Ya yi kira ga al’ummar Wajari da su ɗauki cibiyar a matsayin tasu, su tabbatar da kula da ita yadda ya kamata, tare da yin amfani da ayyukan kiwon lafiyar da ake bayarwa a cikinta.

Bikin ya ƙare da nuna godiya daga al’ummar Wajari ga ma’aikatan CBN bisa wannan gagarumar gudummawa, tare da addu’ar Allah Ya ci gaba da ba su nasara da albarka, da kuma duk waɗanda suka bayar da gudummawa wajen gyaran cibiyar kiwon lafiyar.

Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Dr. Zainab Gwamna Ta Hada Mata Fiye Da 6,000 Domin Haɗin Kai Da Ci Gaba A Gombe
Next Post: Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki

Karin Labarai Masu Alaka

Ghana Tayi Watsi Da Yarjejeniya Akan Hakar Ma’adanai Afrika
Bankin Duniya Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Afirka Da Yankin Sahara Afrika
Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi Najeriya
Hadakar Kungiyoyin Sauyin Yanayi Ta Bukaci ‘Yan Siyasa Su Dauki Matakan Kare Muhalli Afrika
Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC Afrika
  • Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf Ya Gana Da Shugaba Tinubu Siyasa
  • Farashin Kasuwar Yawon Bude Ido A Kasuwar Hannayen Jari Ya Fadi Afrika
  • An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025 Wasanni
  • Za’ayi Auren Zawarawa Dubu Uku A Kano Afrika
  • Kungiyar Cigaban Al’ummar Tangale Tace Bata Goyon Bayan Kai Ziyara Wa Gwamnan Gombe Labarai
  • Margayi Shugaba Muhammadu Buhari 1942-2025 Labarai
  • Magoya Bayan Manchester United Sun Bukaci A Siyar da Bruno Fernandes Bayan Rashin Nasara A Kan AC Milan Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.