Gwamnatin jihar Filato a Najeriya ta bayar da umarnin bude dukkan makarantun firamare da sakandare na gwamnati da masu zaman kansu a jihar daga ranar Litinin 14 ga Satumba, 2026.
Kwamishiniyar yada labarai da sadarwa, Joyce Lohya Ramnap, ce ta sanar da hakan a cikin wata sanarwa a ranar Juma’a, inda ta ce matakin ya biyo bayan matakan riga-kafi da aka dauka domin dakile yaduwar cutar diphtheria wato Mashako wanda ya hallaka yara da dama sassan jihar, yayinda wassu ke jinya a cibiyoyin lafiya a jihar.
Dakta Job Maren, shine shugaban sashen dake kula da cututtuka masu yaduwa a jihar Filato, yace sun lura cewa mafi yawan wadanda suka kamu sa cutar basu yi rigakafi ba.
A makon jiya ne gwamnatin jihar ta Filato ta sanar da rufe makarantu na wani dan lokaci don baiwa hukumomin lafiya damar karfafa ayyukan sa ido kan bullar Diphtheria a wassu kananan hukumomin jihar.
Malam Bala Kwamanda dake garin Bukur a karamar hukumar Jos ta Kudu a jihar Filato ya bukaci iyaye su dau matakan kariya a gida da kuma kan yaransu dake zuwa makarantu.
Gwamnati ta umurci hukumomin makarantu da su kula da tsaftar muhalli da tsaftar dalibai tare da sanya ido sosai don gano alamomin cutar, don samun kulawar gaggawa.
Gwamnati ta kuma shawarci jama’a game da rashin fa’idar yin amfani da magungunan ba’a tantance sahihancinsu ba ko kuma boye wadanda ke da alamun cutar, tana mai jaddada cewa ganowa da kuma magance cutar da wuri na da matukar muhimmanci wajen hana ci gaba da yaduwar curar a tsakanin al’umma.
Ga rahoton Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana a jihar Filato Zainab Babaji


