Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Abun Da Kuke Buƙatar Sani Game Da Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka 2025
Published: December 10, 2025 at 10:08 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 11, 2025

Duk abin da kuke buƙatar sani game da Gasar Cin Kofin kasashen Afirka ta 2025.

Manyan ‘yan wasan ƙwallon ƙafa na Afirka za su nufi Morocco yayin da Gasar Cin Kofin Afirka ta 2025 ta zama gasa ta farko da aka shirya a lokacin Kirsimeti da Sabuwar Shekara.

Masu masaukin baki za su buɗe gasar a ranar Lahadi, 21 ga Disamba, inda za su fafata da Comoros a filin wasa na Prince Moulay Abdellah da ke Rabat da ƙarfe 19:00 GMT.

A jaddawalin Fifa Morocco tana matsayi na 11 a duniya rabon ta ɗaga kofin tun 1976, wannan shine wasa karo na 35.

Ga yadda aka tsara ƙungiyoyin

 

 

 

 

 

Ƙungiyoyin Kwallon Kafa na Ƙasashe ashirin da huɗu (24) za su fafata bisa tsarin rukuni shida (6) a kowani rukuni a kwai huɗu, inda ƙungiyoyi biyu a kowace rukuni tare da ƙungiyoyi huɗu mafi kyau da suka zo na uku za su kai zagaye na 16.

 

 

 

 

 

Rukunin A:

Morocco, Mali, Zambia, Comoros

Rukunin B:
Masar, Afirka ta Kudu, Angola, Zimbabwe

Rukunin C:
Najeriya, Tunisia, Uganda, Tanzania

Rukunin D:
Senegal, DR Congo, Benin, Botswana

Rukunin E:
Algeria, Burkina Faso, Equatorial Guinea, Sudan

Rukunin F:
Ivory Coast, Kamaru, Gabon, Mozambique

Gasar Afcon 2025 Za Ta Fara Ne Kamar Haka:

Wasan farko zai fara da ƙarfe 19:00 GMT a ranar 21 ga Disamba, har zuwa 31 ga Disamba, inda za’a keb buga wasanni huɗu a kowace rana da ƙarfe 12:30 GMT, 15:00 GMT, 17:30 GMT da kuma 20:00 GMT

Wasannin zagayen rukuni na ƙarshe za su fara ne da ƙarfe 16:00 ko 19:00 GMT.

Matakin kihuwa daya kuma (Knockout) zai fara ne a ranar Asabar, 3 ga Janairu, zuwa ranar Lahadi, 18 ga Janairu da ƙarfe 19:00 GMT.

Filayen Da Za’a Buga Wasanni:

Morocco ta gyara filayen wasa a duk faɗin ƙasar don shirye-shiryen gasar AFCON 2025 yayin da take kokarin ganin ta dauki matsayin mai masaukin baki na gasar cin kofin duniya a 2030.

Filaye tara dake fadin birane shida a ƙasar ta Morocco za su karbi bakuncin wasannin, ciki har da guda hudu a Rabat:

Rabat

• Filin wasa na Prince Moulay Abdellah mai daukan mutum (69,500)

 

 

 

 

 

 

­Filin wasa na Complexe Sportif Prince Moulay Abdellah Olympic mai daukar mutum (21,000)

• Complexe Sportif Prince Heritier Moulay El Hassan mai daukar mutum (22,000)

• Stade El Barid mai daukar mutum (18,000)

• Grande Stade d’Agadir, Agadir mai daukar mutum (45,480)

• Complexe Sportif de Fes, Fes mai daukar mutum (45,000)

• Grande Stade de Marrakech, Marrakech mai daukar mutum (45,240)

• Stade Mohammed V, Casablanca mai daukar (67,000)

• Grande Stade de Tangier, Tangier mai daukar mutum (68,000)

Inda za’a buga wasan karshe a Rabat.

Cikakken Wasannin Na Afcon An Tsara Shi Kamar Haka:

Lahadi, 21 ga Disamba

Rukunin A: Morocco da Comoros, Rabat (19:00)GMT

Litinin, 22 ga Disamba

Rukunin A: Mali da Zambia, Casablanca (14:00)GMT

Rukunin B: Afirka ta Kudu da Angola, Marrakech (17:00)GMT

Rukunin B: Masar da Zimbabwe, Agadir (20:00)GMT

Talata, 23 ga Disamba

Rukunin D: Senegal da Botswana, Tangier (12:30)GMT

Rukuni D: DR Congo da Benin, Rabat (15:00)GMT

Rukunin C: Najeriya da Tanzania, Fes (17:30)GMT

Rukunin C: Tunisia da Uganda, Rabat (20:00)GMT

Laraba, 24 ga Disamba

Rukunin E: Burkina Faso da Equatorial Guinea, Casablanca (12:30)GMT

Rukunin E: Algeria v Sudan, Rabat (15:00)GMT

Rukunin F: Ivory Coast v Mozambique, Marrakech (17:30)GMT

Rukunin F: Kamaru da Gabon, Agadir (20:00)GMT

Juma’a, 26 ga Disamba

Rukunin B: Angola da Zimbabwe, Marrakech (12:30)GMT

Rukunin B: Masar da Afirka ta Kudu, Agadir (15:00)GMT

Rukunin A: Zambia v Comoros, Casablanca (17:30)GMT

Rukunin A: Morocco da Mali, Rabat (20:00)GMT

Asabar, 27 ga Disamba

Rukuni na D: Benin da Botswana, Rabat (12:30)GMT

Rukunin D: Senegal v DR Congo, Tangier (15:00)GMT

Rukunin C: Uganda da Tanzania, Rabat (17:30)GMT

Rukunin C: Najeriya da Tunisia, Fes (20:00)GMT

Lahadi, 28 ga Disamba

Rukunin F: Gabon da Mozambique, Agadir (12:30)GMT

Rukunin E: Equatorial Guinea da Sudan, Casablanca (15:00)GMT

Rukunin E: Algeria da Burkina Faso, Rabat (17:30)GMT

Rukunin F: Ivory Coast da Kamaru, Marrakech (20:00)GMT

Litinin, 29 ga Disamba

Rukunin B: Angola da Masar, Agadir (16:00)GMT

Rukunin B: Zimbabwe da Afirka ta Kudu, Marrakech (16:00)GMT

Rukuni A: Comoros da Mali, Casablanca (19:00)GMT

Rukunin A: Zambia v Morocco, Rabat (19:00)GMT

Talata, 30 ga Disamba

Rukunin C: Tanzania da Tunisia, Rabat (16:00)GMT

Rukunin C: Uganda da Najeriya, Fes (16:00)GMT

Rukunin D: Benin da Senegal, Tangier (19:00)GMT

Rukunin D: Botswana da DR Congo, Rabat (19:00)GMT

Laraba, 31 ga Disamba

Rukunin E: Equatorial Guinea da Algeria, Rabat (16:00)GMT

Rukunin E: Sudan v Burkina Faso, Casablanca (16:00) GMT

Rukunin F: Gabon da Ivory Coast, Marrakech (19:00) GMT

Rukunin F: Mozambique da Kamaru, Agadir (19:00)GMT

Mataki na ƙarshe

Zagaye ƙungiyoyi 16 – Kuma Za’a Fara 3 zuwa 6 Janairu

Asabar, 3 ga Janairu

SR1: Na daya a rukuni D v da na 3 a rukunin B/E/F, a filin Tangier (16:00) GMT

SR2: Wanda ya zo na daya a rukunin A v da na biyu a rukunin C, Casablanca (19:00) GMT

Lahadi, 4 ga Janairu

SR3: Wanda ya zo na daya a rukunin A v da na 3 daga rukunin C/D/E, Rabat (16:00)GMT

SR4: Wanda ya zo na daya a rukunin B v da na biyu a rukunin F, Rabat (19:00)GMT

Litinin, 5 ga Janairu

SR5: Wanda ya zo na daya a rukuni B v da na 3 daga rukunin A/C/D, Agadir (16:00) GMT

SR6: Wanda ya zo na daya a rukuni C v da na 3 a rukunin A/B/F, Fes (19:00) GMT

Talata, 6 ga Janairu

SR7: Wanda ya zo na daya a rukunin E v da na biyu a rukunin D, Rabat (16:00)GMT

SR8: Wanda ya zo na daya a rukuni F da wanda ya zo na biyu a rukunin E, Marrakech (19:00) GMT

Wasan kusa da na kusa da na karshe – Ranar 9 & 10 Janairu

Juma’a, 9 Janairu

QF1: Wanda ya nasara a a wasan SR2 da wanda ya yi nasara a SR1, Tangier (16:00)GMT

QF2: Wanda ya yi nasara a SR4 da wanda ya yi nasara a SR3, Rabat (19:00)GMT

Asabar, 10 ga Janairu

QF3: Wanda ya yi nasara a SR7 da Wanda ya yi nasara a SR6, Marrakech (16:00) GMT

QF4: Wanda ya yi nasara a SR5 da Wanda ya yi nasara a SR8, Agadir (19:00) GMT

Wasan daf da na karshe – 14 ga Janairu

SF1: Wanda ya yi nasara a QF1 da Wanda ya yi nasara a QF4, Tangier (17:00) GMT

SF2: Wanda ya yi nasara a QF3 da Wanda ya yi nasara a QF2, Rabat (20:00) GMT

Wasan neman matsayi na uku – 17 ga Janairu
Casablanca (16:00)GMT

Rabat (19:00)GMT

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato
Next Post: Sarkin Musulmi Yayi Magana Game Da Matsalar Tsaron Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Oliseh, Ya Ba Eric Chelle, Shawara Da Ya Zamo Mai Tsauri AFCON 2025. Wasanni
Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora Wasanni
Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni
Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
Onana Ba Ya Cikin Tawagar Kamaru (AFCON) Wasanni
Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakuncin Wasannin Afirka Na 2031. Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike a Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakuncin Wasannin Afirka Na 2031.
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • FIFA Na Shirin Fadada Babban Na’urar VAR A Gasar Cin Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Za’a Dauko Messi Aro Zuwa Barcelona Deco Wasanni
  • Ukraine Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Tsarin Cimma Yarjejeniya Sauran Duniya
  • Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
  • An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa Tsaro
  • Sojoji Sun Murkushe ‘Yan Bindiga A Jihar Sakkwato Labarai
  • Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
  • Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.