Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zamu Hana Wasu ‘Yan-Najeriya Visa Shiga Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa
Published: December 17, 2025 at 3:29 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 17, 2025

Tsohon kyaftin ɗin Super Eagles Ahmed Musa ya sanar da yin ritaya daga ƙwallon ƙafa ta ƙasa da ƙasa, wanda hakan ya kawo ƙarshen shekaru 15 da ya shafe yana wasa wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Najeriya.

Musa ya sanar da hakan ne a ranar Laraba ta shafin X ɗinsa a hukuma, yana mai bayyana shawarar tasa ta biyo bayan la’akari da ya yi sosai, ya ce sanya rigar kore da fari idan ya tuna abu ne mai ma’ana sosai a gare shi.

Na tuna lokacin da na fara tafiya ta ƙasa da ƙasa a matsayin matashin ɗan wasa, lokacin da aka gayyace ni zuwa ƙungiyoyin ƙasa na ‘yan ƙasa da shekaru 20, da 23 da manyan ƙungiyoyi, ban taba yin jinkirin zuwa Najeriya ba” in ji shi.

Musa ya ya buga wasanni 111 a ƙungiyar Super Eagles, wanda hakan ya sa ya zama ɗan wasa mafi buga wasa a tarihin ƙwallon ƙafa ta ƙasar.

Ya samu nasarar lashe gasar cin kofin ƙasashen Afirka ta 2013 kuma ya ci gaba da zama ɗan wasan da ya fi zura ƙwallo a Najeriya a gasar cin kofin duniya ta FIFA, inda ya zura ƙwallaye masu kyau a kan Argentina a 2014 da Iceland a 2018.

Ya bayyana cimma wasanni 111 a matsayin babban abin farin ciki da girmamawa ne a koyaushe.

Musa ya ƙara da cewa lashe gasar AFCON ta 2013 wani muhimmin abu ne, zaman kyaftin ɗin ƙungiyar ya koya masa darussa masu mahimmanci game da shugabanci, haƙuri da kuma sanya wasu a gaba.

Babban Manaja kuma ɗan wasan ƙungiyar Kano Pillars ya gode wa abokan aikinsa, masu horarwa, da duk ma’aikatan da kuma masu kula da ƙwallon ƙafa saboda goyon bayan da suka ba shi na tsawon shekaru.

Ya kuma nuna matuƙar godiya ga magoya bayan Najeriya na gida da waje saboda alakar da sukayi da shi a tsawon aikinsa.

Ya kammala da cewa ya ba da dukkanin iyawarsa ga Najeriya kuma yana da kwarin gwiwa game da makomar Super Eagles, ya ƙara da cewa dangantakarsa da ƙasar za ta ci gaba.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar
Next Post: Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu

Karin Labarai Masu Alaka

Lawal, Filin Wasa Na Rashidi Yekini Ko Turai Iyaka Wasanni
Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
‘Yan-Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Daliban St. Mary! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya Wasanni
An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya
  • Fiye Da Fararen Hula 1000 Yunwa Ta Kashe A Sudan
  • Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Gabatar Da Kudi Fiye Da Naira Triliyan 58 A Matsayin Kasafin 2026
  • Zamu Hana Wasu ‘Yan-Najeriya Visa Shiga Amurka

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi Labarai
  • ‘Yan Sanda Sunce Mutum Daya Ne Yakai Hare-Haren Jami’ar Brown Da Kuma Na MIT Boston Amurka
  • Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza Labarai
  • Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya
  • Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni
  • Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
  • Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.