Azumi lokaci ne na sadaukar da kai ga ibada, nuna tausayi ga wadanda ke cikin kunci.
A yayinda al’ummar musulmi suka tashi da azumin watan Ramadan a wannan Laraba, suma mabiya addinin Kirista sun tashi da azumi na kwanaki arba’in da ake kira Lent.

Malam Abdullahi Usman Abubakar, shine Ladanin babban masallacin Jos, yace azumi na sanya talaka da attajiri su kasance cikin yanayi guda.
Shima Rabaran Fada Bulus Dalyop na Fatima cathedral Jos yace azumi na Lent lokaci ne na yin nazarin rayuwa da kusanci da Allah.
Ahmed Ibrahim Tigana yace hadewar ranar fara azumin na nuna alamar zaman lafiya.
Shima Mr Johnson ya bukaci jama’a su kasance da imani.
Al’ummar Musulmi da Kiristan dai sun yi alkawarin yin addu’oi don samun zaman lafiya da karuwar Cigaba a Najeriya.
Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton


