Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma
Published: December 8, 2025 at 4:42 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

A karon farko tun bayan da gwamnatin Nijar ta kudiri aniyar maka kamfanin Orano a kotu, kungiyoyin farar hula a kasar sun jaddada goyon baya kan abin da suka kira yunkurin kwato ‘yancin a kan sha’anin ma’adanai.
Kungiyoyin sun kuma shawarci hukumomin na Nijar da su janye lasisin hakar zinare daga hannun kamfanonin da suka yi kaka-gida don mayar da komai a hannun ‘yan kasa.
A wata sanarwar da ta fitar ne kungiyar M62 ta bayyana matsayinta dangane da kace nacen da ya taso a tsakanin hukumomin Nijar, da kamfanin Orano na Faransa bayan da Nijar ta fara kwashe ton ton na Uranium din da ke jibge shekaru sama da biyu a garin Arlit.
Kungiyar tace ta na goyon matakin da gwamnatin Nijar ta dauka, wanda ta ke ganinsa tamkar matakin kawo karshen mulkin mallakar da aka shafe shekaru fiye da 60 a na yi wa kasar harakar Uranium. Falmata Taya na daga cikin shugabanin M62.
Ita ma kungiyar FRSA mai da’awar kwato ‘yancin kai Afirka a sanarwar da ta bayar ta bayyana gamsuwa da abin da ta kira sabon babin da gwamnatin Abdourahamane Tiani ta bude a fannin ma’adanan karkashin kasa. Salissou Ibrahim shine sakataren watsa labaran kungiyar.
Ko baya ga harakar Uranium kungiyar M62 na ganin bukatar gwamnatin Nijar ta fadada sauye sauyen da ta fara zuwa sha’anin hakar zinare.
Mahawwara kan hurumin fitar da Uranium zuwa waje a tsakanin gwamnatin Nijar da kamfanin Orano na Faransa na ci gaba da karfafa ne a wani lokacin da bangarorin biyu ke jiran hukuncin kotun CIRDI dangane da makomar ton 1300 na Uranium da ke girke a yankin arewacin Nijar.
M62 ta bukaci hukumomin kasar su gudanar da bincike kan illahirin aiyukan bankin duniya saboda alakarsu da kotun CIRDI.
Afrika

Post navigation

Previous Post: An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa
Next Post: “Hotuna” An Sako Daliban Makarantar St. Mary’s Su 100

Karin Labarai Masu Alaka

Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu Afrika
Amurka Ta Gabatarwa Sassan Dake Yakar Juna A Sudan da Shirin Tsagaita Wuta Afrika
Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika
Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika
Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum Afrika
Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike a Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakuncin Wasannin Afirka Na 2031.
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Gwamna Bala Kauran Bauchi Yace Yana Nan Daram a Jam’iyar PDP Siyasa
  • Bana Ba Harka Ga ‘Yan-Wasan Kwallon Kafar Najeriya Wasanni
  • Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar Najeriya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s Tsaro
  • Kasar Congo Ta Dau Alwashin Bin Tsari Wajen Rarraba Ma’adanai Afrika
  • Umar Ya Lashe Kyautar Gwarzon ‘Dan-Wasa Na 2025 Wasanni
  • Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
  • Oliseh, Ya Ba Eric Chelle, Shawara Da Ya Zamo Mai Tsauri AFCON 2025. Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.