Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka

Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano
Published: December 13, 2025 at 3:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 13, 2025

Gwamnatin Kano ta umarci jami’an tsaro su dakatar da masu yunkurin kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta.

Gwamnatin Jihar Kano ta fitar da umarnin zantaswa da ya haramta wata kungiya da ke aiki da sunan “Independent Hisbah Fisabilillahi” Wannan umarni da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanya wa hannu, mai dauke da ranar 8 ga Disamba, 2025, ya bayyana cewa gwamnati ta gano cewa ana ci gaba da daukar ma’aikata, horaswa da tura matasa cikin kungiyar ba tare da wata doka ko izini ba, kana kuma cikin sabawa dokar Hukumar Hisbah ta Jihar Kano.

Yayin da yake mika sakon ga manema labarai, Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya bayyana cewa Hukumar Hisbah ce kadai hukuma ta doka da ke da ikon jagorantar dukkan ayyukan Hisbah a fadin jihar.

Gwamnati ta ce bullar wannan kungiya ta daban wani yunkuri ne na kafa wata hukuma ba bisa ka’ida ba, lamarin da zai iya haifar da tashin hankali da kuma take matsayin hukumar Hisbah ta jihar.

Gwamnan ya kuma bayyana dukkan ayyukan kungiyar a matsayin “haramtattu, ba bisa doka ba kuma babu inganci,” yana gargadin cewa duk wani kaya da ya yi kamanceceniya da alamomi ko ikon Hukumar Hisbah zai fuskanci hukunci.

Gwamna Yusuf ya umarci Rundunar ‘Yansanda ta Najeriya, Hukumar DSS, NSCDC da sauran hukumomin tsaro da su binciki wadanda ke goyon bayan kungiyar, su dakatar da duk wani ci gaba da ake yi na daukar ma’aikata ko horaswa, sannan su dauki matakan da suka dace don hana tabarbarewar tsaro a jihar Kano.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina
Next Post: Anyi Jefe-Jefe Yayin Rangadin Messi, A Indiya

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kungiyar Cigaban Al’ummar Tangale Tace Bata Goyon Bayan Kai Ziyara Wa Gwamnan Gombe Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati Labarai
  • Amurka Zata Bawa Ukraine Tsaro Na Musamman Amurka
  • NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari Labarai
  • Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade Najeriya
  • Shugabar Hamayya A Venezuela Ta Gana Da Paparoma Leo Amurka
  • Libya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashen Faransa Da Amurka Afrika
  • Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.