Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano
Published: December 13, 2025 at 3:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 13, 2025

Gwamnatin Kano ta umarci jami’an tsaro su dakatar da masu yunkurin kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta.

Gwamnatin Jihar Kano ta fitar da umarnin zantaswa da ya haramta wata kungiya da ke aiki da sunan “Independent Hisbah Fisabilillahi” Wannan umarni da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanya wa hannu, mai dauke da ranar 8 ga Disamba, 2025, ya bayyana cewa gwamnati ta gano cewa ana ci gaba da daukar ma’aikata, horaswa da tura matasa cikin kungiyar ba tare da wata doka ko izini ba, kana kuma cikin sabawa dokar Hukumar Hisbah ta Jihar Kano.

Yayin da yake mika sakon ga manema labarai, Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya bayyana cewa Hukumar Hisbah ce kadai hukuma ta doka da ke da ikon jagorantar dukkan ayyukan Hisbah a fadin jihar.

Gwamnati ta ce bullar wannan kungiya ta daban wani yunkuri ne na kafa wata hukuma ba bisa ka’ida ba, lamarin da zai iya haifar da tashin hankali da kuma take matsayin hukumar Hisbah ta jihar.

Gwamnan ya kuma bayyana dukkan ayyukan kungiyar a matsayin “haramtattu, ba bisa doka ba kuma babu inganci,” yana gargadin cewa duk wani kaya da ya yi kamanceceniya da alamomi ko ikon Hukumar Hisbah zai fuskanci hukunci.

Gwamna Yusuf ya umarci Rundunar ‘Yansanda ta Najeriya, Hukumar DSS, NSCDC da sauran hukumomin tsaro da su binciki wadanda ke goyon bayan kungiyar, su dakatar da duk wani ci gaba da ake yi na daukar ma’aikata ko horaswa, sannan su dauki matakan da suka dace don hana tabarbarewar tsaro a jihar Kano.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina
Next Post: Anyi Jefe-Jefe Yayin Rangadin Messi, A Indiya

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutu Najeriya
Mabiya Addinin Kirista Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Sun Kubuta Labarai
Putin, Sakon Sabuwar Shekara Ya Jinjinawa Dakarun Rasha Da Suke Yaki A Ukraine Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ministan Kudin Najeriya: Bamu Samu Kudaden Da Muke Tsammani A Wannan Shekarar Ba Najeriya
Ganduje Ne Yasa Aka Kama Ni Inji Muhuyi Magaji Najeriya
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe Kiwon Lafiya
  • An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Don Neman Zaman Lafiya Labarai
  • China Ta Dawo Da Harajin Magungunan Hana Haihuwa Labarai
  • Kamfanin Jiragen Saman Ethiopia Zai Kafa Babban Filin Jirgi Afrika
  • Gwamnatin Sojan Burkina Faso Ta Soke Jam’iyyun Siyasar Kasar Afrika
  • An Kama Maharan Bom Din Maiduguri Tsaro
  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna Najeriya
  • An Gano Kwale-Kwalen Fir’auna A Birnin Masar Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.