Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Kano Ta Rufe Gidajen Bukukuwa Da Shakatawa
Published: February 18, 2026 at 4:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar tace fina-finai ta jihar Kano ta bada da umarnin rufe dukkan wuraren bukukuwa wato event centre da na shaƙatawa a fadin jihar.

Hakazalika hukumar ta hana kidan DJ da kuma gidajen gala yayin da aka fara azumin watan Ramadan.

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ne ya sanar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata.

“Daga ranar Laraba, 18 ga Fabrairu, 2026, duk irin waɗannan wurare (cibiyoyin nishaɗi) za su kasance a rufe har zuwa ƙarshen watan Ramadan mai alfarma.

“Umarnin zai fara aiki daga ƙarfe 10:00 na dare a ranar (Laraba),” in ji sanarwar.

A cewar hukumar, an ɗauki matakin ne domin bai wa al’umma damar gudanar da azumin Ramadan da ayyukan ibadarsu cikin kwanciyar hankali ba tare da wata katsalandan ba.

Sanarwar ta ƙara da cewa rufewar za ta ci gaba a duk tsawon lokacin azumi, yayin da za a sanar da ranar sake buɗe wuraren, musamman a lokacin bukukuwan Sallah, a lokacin da ya dace.

Hukumar ta buƙaci dukkan masu ruwa da tsaki su ba da cikakken haɗin kai tare da bin umarnin bisa dokar da ta kafa ta.

Ta kuma jaddada cewa matakin na daga cikin aikinta na tabbatar da bin ƙa’idojin da suka shafi harkokin nishaɗi a jihar.

Hukumar ta yi addu’ar Allah Ya ba da zaman lafiya da lafiya a lokacin gudanar da ibadar watan mai alfarma, tare da roƙon Allah Ya sa kowa ya shaida watan cikin rahama da arziki.

Labarai, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci
Next Post: Shugaba Bola Tinubu Ya Saka Hannu A Dokar Zabe

Karin Labarai Masu Alaka

Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne Labarai
Yanbindiga sun Kashe kimanin mutane 30 a yankin kayama ta Jihar kwaran Najeriya Najeriya
Hukumar Zabe A Najeriya Ta Cigaba Da Rijistar Katin Zabe Labarai
Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura Labarai
Fadar Sarkin Musulmi: Talata Ne 1 Ga Watan Sha’aban Na 1447AH Najeriya
Gwamnatin Tarayya: Bikin Al’adun Argungu Ya Karbu A Idon Duniya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Farashin Mai A Kasuwannin Duniya Yayi ƙasa Kadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina Najeriya
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi Afrika
  • Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ADC Ta Sha Damarar Gwabzawa Da APC A Zaben 2027 Shirye-Shirye
  • An Hana Yada Rahotannin Siyasa A Kasar Uganda Tsaro
  • Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.