Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai

Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro
Published: December 14, 2025 at 5:35 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya kafa rundunar kar-ta-kwana domin ƙarfafa tsaro a tashoshin mota da sauran muhimman wuraren taruwar jama’a a faɗin jihar.

Wannan na cikin sanarwar da Daraktan Yada Labaran gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Lahadi 14 ga Disamba 2025.

Sanarwar ta ce an ɗauki matakin ne domin dakile shigowar masu aikata laifuka, musamman a wuraren da ake yawan zirga-zirga, ciki har da tashoshin mota da wuraren shigowa da fita daga birnin Kano.

Rundunar kar-ta-kwanan za ta riƙa sa ido, tattara bayanan sirri da aiwatar da ayyukan tsaro tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro, domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Sanarwar ta ƙara da cewa aikin rundunar zai shafi har da gidajen mai da sauran wuraren taruwar jama’a da ake ganin zai iya haifar da barazanar tsaro.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro
Next Post: Abu Mafi Daukar Hankali A Wasan Dambe Na Yau

Karin Labarai Masu Alaka

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno Tsaro
Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro Tsaro
EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi Tsaro
Shugaba Tinubu Ya Umarci Janye ‘Yan Sanda Masu Gadin Ministoci Tsaro
Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya
  • Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani
  • Hukumar NAPTIP ta Kubutar da Yara 11 daga Hannun Masu Safara Mutane
  • Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina
  • Dangote Ya Rage Farashin Mai A Najeriya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5 Labarai
  • An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu Afrika
  • Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne Labarai
  • Trump Da Bin Salman Da Wasu Kasashe Za Su Sa Hannu A Rikicin Sudan Labarai
  • AFCON ChelIe, Ya Fidda Sunayen ‘Yan Wasan Super Eagles Na Karshe. Wasanni
  • Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba Najeriya
  • Sojojin Kasar Isra’ila Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Hamas Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.