Jam’iyyar APC Mai Mulki a Najeriya tarantsar da sabbin Shugaban ta a Jihar Neja dake Arewa Maso tsakiyar kasar,
Akasarin wadanda ke rike da shugaban cin Jam’iyyar ne aka sake rantsarwa saboda yin sulhu a tsakanin masu Neman Shugaban cin APC a Jihar Neja,
Alhaji Aminu Musa Bobi shine aka sake rantsarwa a matsayin sabon shugaban APC da zai kara wa’adi na biyu,
Mataimakin Shugaban APC na kasa Mai Kula da shiyyar Arewa maso tsakiyar Najeriya Alhaji Mu’azu Bawa yace bayan kammala zaben Shugabannin APC na kananan Hukumomin jihar Nejan cikin Nasara yau kuma gashi za’a rantsar da Shugaban ni na Jiha ba tare da wata Matsala ba.
Tsohon Gwamnan Jihar Neja Sanata Abubakar Sani Bello da ya halarci taron ya yaba da yadda zaben ya gudana.
Yace sau dayawa Idan za’ayi zaben Shugabannin jam’iyya ya kanzo da Matsala Amma ka duba Wannan kowa yana cikin Fara’a Saboda haka muna yabawa Gwamna kuma muna tayashi murna.
To Gwamna Umar Bago Yace sunji dadi akan yadda zaben ya gudana.

Anan gaba kadan ne dai APC zata Gudanar da Babban Taron ta na kasa Domin Zaben Sabbin Shugaban ni gabanin zuwan Babban zaben Shekara ta 2027 da jam,iyyun Adawa suma suke shirin ganin sunyi Nasarar kawar da APC daga madafun iko.
Wakilin GTA Hausa Amurka Ke Magana Mustapha Nasiru Batsari dauke da cikekken rahoton Daga Minna


