Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Karo Na Biyu Cikin Kwanaki 29 An Samu Gobara A Kasuwar Katako
Published: December 16, 2025 at 11:04 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 16, 2025

Wakilin GTA Hausa “Amurka Ke Magana” a Gombe, Aliyu Bala Gerengi, ya rawaito cewa gobarar ta tashi ne a daren ranar Litinin, inda ake zargin matsalar lantarki ce ta haddasa ta, lamarin da ya jawo konewar shaguna da dama da kuma kayayyaki da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

Wannan iftila’i ya faru ne kwanaki 29 kacal bayan da wani ɓangare na kasuwar, musamman sashen tsofaffin ƙarafa da soso (scrap da metal), ya ƙone a ranar 17 ga Nuwamba, inda gobarar ta lalata shaguna fiye da 30 tare da dukiyoyi da aka kiyasta darajarsu ta haura naira miliyan 500.

A daren Litinin ɗin, wani ɓangare na kasuwar ya sake kamawa da wuta, abin da ya ƙara tsananta asarar da ’yan kasuwar suka tafka, musamman waɗanda itace kawai hanyar cin abincin su.

Amma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ba da umarnin gudanar da bincike kan gobarar da ta tashi a kasuwar katako a jihar, wacce ta ƙone shaguna da kayayyaki masu yawa, lamarin da ya janyo asarar dukiya mai yawa ga ‘yan kasuwa da dama.

Gwamnan Inuwa Yahaya, ya bayyana alhini da jimami matuƙa bisa faruwar wannan lamarin.

A cikin wata sanarwa da Darakta-janar na harkokin yaɗa labarai na gwamnatin jihar, Ismaila Uba Misilli, ya fitar, gwamnan ya bayyana lamarin a matsayin babban rashi da juyayi ga al’ummar da abin ya shafa, tare da miƙa saƙon jaje ga dukkan ‘yan kasuwa da masu shagunan da gobarar ta rutsa da su.

Sanarwar ta ce “Gwamna Inuwa ya tabbatar wa waɗanda abin ya shafa cewa gwamnatin jihar tana tare da su a wannan lokaci na radadi, inda ya umarci hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar wato (SEMA) da sauran hukumomi masu alaƙa da su da su hanzarta bincike kan musabbabin gobarar, tare da kai tallafi da agajin gaggawa ga waɗanda abin ya shafa.

Gwamnan ya kuma jaddada ƙudirin gwamnatinsa na kafa wata cibiyar kwana-kwana ta zamani mai kayan aiki da ƙwarewa domin ƙarfafa kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71
Next Post: Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar Hasashen Kasuwanci Na Zargin Saida Bayanan Sirri Amurka
Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
Tattalin Arzikin Kasar Uganda Zai Bunkasa A Wannan Shekarar Labarai
Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia Afrika
Sojojin Faransa Sun Karyata Zargin Bobi Wine Labarai
Jami’ai A Mexico Sun Tabbatar Da Kashe Shugaban Masu Shan Ƙwaya Nemesio Oseguera Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
  • Sakamakon Rikicin Gabas Ta Tsakiya Farashin Mai Ya Karu Labarai
  • Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
  • Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika
  • Ansamu Maganin Da Yake Rage Kitsen Jijiyoyi A Amurka Amurka
  • Rasha Ta Nuna Kudurin Cimma Zaman Lafiya Da Ukraine Amurka
  • Zulum Ya Rushe Majalisar Zartarwa Ta Jihar Borno Afrika
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Yi Ma Wasu Mutane Yankan Rago A Jihar Neja Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.