Ranar Asabar Majalisar dokokin kasar Kamaru ta amince da gagarumin rinjaye sake kirkiro da ofishin mataimakin shugaban kasa, mataki da gwamnatin tace zai sa a sami dorewa a tafiyar da harkokin gwamnati, amma ‘yan hamayya suka bayyana matakin a zaman karawa Barno doki ne ga bangaren zartaswa.
A wani zaman hadin guiwar majalisun kasar da jam’iyyar dake mulkin kasar take da rinjaye a majalisar dattijai data wakilai, ‘yan majalisa metan ne suka amince da kudurin, wakilai 18 suka ki amincewa, mutum hudu suka ki kada kuri’a.
Dokar ta ayyana cewa, mataimakin shugaban kasar kai tsaye zai maye gurbin shugaban kasa, idan shugaba Paul Biya ya rasu, ko yayi murabus, ko kuma ya fada wani hali ko yanayi da zai hana shi tafiyarda aikinsa.
Shugaba Paul Biya mai shekaru 93 da haifuwa, shi yake jagorancin kasar dake yankin Afirka ta tsakiya tun a shekarar 1982, kuma shine shugaban kasa mafi shekaru a duniya. An haramta magana kan lafiyarsa a kasar.


