Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya
Published: December 14, 2025 at 2:37 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC), Kwamared Joe Ajaero, ya yabawa Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa irin kulawa da tabbatar da jin daɗin ma’aikata a jihar.

Ajaero ya bayyana hakan yayin wani taron da ya gudana, inda ya ce ko da yake ƙungiyar ba ta cika yawan yabon gwamnoni ba, amma Gwamna Inuwa Yahaya ya cancanci yabo bisa irin yadda yake baiwa ma’aikata muhimmanci da kuma cika alƙawurra.

Saboda haka, NLC ta karrama Gwamna Inuwa da lambar yabo ta “Gwamna Mai Ƙaunar Ma’aikata”, a matsayin wanda ke da kyakkyawar dangantaka da ma’aikatansa tare da ɗaukar walwalarsu a matsayin fifiko.

Wannan karramawa na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Gombe ke ci gaba da aiwatar da manufofi da tsare-tsare da suka shafi ci gaban ma’aikata da inganta rayuwar su kamar aiwatar da mafi karancin albashi da kuma aza tubalin gida ofishin sakatariyar kwadago.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Jirgin Sama Ya Fadi A Kano
Next Post: Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya
Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas Najeriya
Shugaba Tinubu Ya Isa Legas Domin Hutun Karshen Shekara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Matatar Man Dangote Ta Samu Tagomashi Daga Abokan Hulda Najeriya
Wike: Bazamuyi Sake Fubara Ya Sake Samun Nasara Ba Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Bassirou: Tawagar Senegal Zasu Samu Kyautar Kudi Da Filaye Sakamakon Nasarar Da sukayi AFCON 2025 Wasanni
  • Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
  • Menene Illar Yada Labaran Karya A Kafofin Sada Zumunta Na Zamani Labarai
  • Jirgin Sojojin Ruwa Yayi Gobara A Cross River Najeriya
  • ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayin Shanu Tsaro
  • Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin Afrika
  • Mabiya Addinin Kirista Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Sun Kubuta Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.