Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai

NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya
Published: December 14, 2025 at 2:37 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC), Kwamared Joe Ajaero, ya yabawa Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa irin kulawa da tabbatar da jin daɗin ma’aikata a jihar.

Ajaero ya bayyana hakan yayin wani taron da ya gudana, inda ya ce ko da yake ƙungiyar ba ta cika yawan yabon gwamnoni ba, amma Gwamna Inuwa Yahaya ya cancanci yabo bisa irin yadda yake baiwa ma’aikata muhimmanci da kuma cika alƙawurra.

Saboda haka, NLC ta karrama Gwamna Inuwa da lambar yabo ta “Gwamna Mai Ƙaunar Ma’aikata”, a matsayin wanda ke da kyakkyawar dangantaka da ma’aikatansa tare da ɗaukar walwalarsu a matsayin fifiko.

Wannan karramawa na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Gombe ke ci gaba da aiwatar da manufofi da tsare-tsare da suka shafi ci gaban ma’aikata da inganta rayuwar su kamar aiwatar da mafi karancin albashi da kuma aza tubalin gida ofishin sakatariyar kwadago.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Jirgin Sama Ya Fadi A Kano
Next Post: Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC

Karin Labarai Masu Alaka

Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya
Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba Kiwon Lafiya
Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ECOWAS Zata Kafa Rundunar Yaki Da Rashin Tsaro
  • Abu Mafi Daukar Hankali A Wasan Dambe Na Yau
  • Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro
  • Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro
  • Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Rasha Na Cigaba Da Kai Hare-Haren Makamai Masu Linzami Ga Ukrain Labarai
  • Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
  • Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
  • Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.