Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja
Published: December 8, 2025 at 7:24 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mai bada Shawara kan Tsaro ga Shugaban Ƙasa (NSA), Malam Nuhu Ribadu, ya mika dalibai 100 na makarantar St. Mary Catholic School da ke Papiri, karamar hukumar Agwara a jihar Neja, ga gwamnatin jihar bayan ceto su daga hannun masu garkuwa da mutane.

An gudanar da mika su a Minna a ranar Litinin, inda Wing Cdr. Abdullahi Idi Hong ya wakilci Nuhu Ribadu wajen gabatar da su ga gwamnatin jihar.

Hong ya ce ceton ya biyo bayan makonni na tsauraran hare haren hadin gwiwa tsakanin ofishin mai bawa shugaban kasa Shawara ta fannin tsaro, Hukumar DSS, Rundunar Sojin Najeriya da sauran hukumomin tsaro.

Ya bayyana cewa DSS ta taka “muhimmiyar rawa ta zahiri” a aikin da ya tabbatar da dawowar yaran cikin koshin lafiya.

Ya kara da cewa ofishin Nuhu Ribadu ya fara samar da matakan gaggawa na tsaro a yankunan da ke fuskantar barazana, tare da hadin gwiwar gwamnatocin jihohi, shugabannin gargajiya da na addini domin samar da tsarin tsaro mai dorewa.

Hong ya jaddada cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da aiwatar da manufofin da ke nufin tabbatar da tsaro a makarantu domin kare hakkin kowane yaro ya samu ilimi cikin kwanciyar hankali.

Da yake jawabi, Gwamna Umaru Bago ya bayyana wannan rana a matsayin “muhimmiya a tarihin jihar Neja,” inda ya gode wa Shugaba Bola Tinubu bisa tallafin da ya bai wa hukumomin tsaro wajen cimma nasarar dawo da yaran.

Haka kuma ya yi godiya ga ofishin mai bawa shugaban kasa shawara ta fannin tsaro, jami’an tsaro, hukumomi da al’ummar jihar da suka yi addu’o’i a lokacin da yaran ke hannu.

Gwamnan ya bayyana kwarin gwiwa cewa sauran daliban da har yanzu ke hannun masu garkuwa za a kubutar da su ba da jimawa ba.

Ya tabbatar wa iyaye cewa za a mika yaran ga iyalansu bayan cikakken binciken lafiya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida
Next Post: Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot.

Karin Labarai Masu Alaka

Fafaroma Leo Zai Ziyarci Kasashen Afirka Amurka
Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika
Pakistan Zata Karbi Tattaunawar Rikicin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Takaddama Ta Barke Tsakanin Lebanon Da Isra’ila Akan Bakin Iyaka Labarai
Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC Afrika
Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Boko Haram Ta Kai Hari Maiduguri Cikin Dare Afrika
  • Kasar China Ta Daina Bada Bashi Da Dalar Amurka Sai Da Kudin Kasar Yuan Labarai
  • Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
  • Thailand Da Cambodia Sun Fara Tattauunawa Kan Batun Tsagaita Wuta Labarai
  • Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai
  • An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
  • Fiye Da Fararen Hula 1000 Yunwa Ta Kashe A Sudan Afrika
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe  Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.