Shugaban ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu, ya amince da shirin biyan bashin naira tiriliyan 3.3 domin warware tsofaffin basussukan da suka daɗe suna addabar ɓangaren wutar lantarki a Najeriya.
Sanarwar daga fadar shugaban ƙasar ta ce bashin ya taru ne daga shekarar 2015 zuwa 2025, kuma an cimma yarjejeniya kan adadin domin kawo ƙarshen matsalar cikin gaskiya.
A sanarwar da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ya fitar ya ce, an riga an fara aiwatar da shirin, inda kamfanonin samar da wuta 15 suka rattaba hannu kan yarjejeniyar biyan naira tiriliyan 2.3, yayin da gwamnati ta tara naira biliyan 501, ciki har da biliyan 223 da aka riga aka biya.
Mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin makamashi, Olu Arowolo-Verheijen, ta ce shirin zai taimaka wajen daidaita harkar wuta, ƙara amincewa, da inganta samar da lantarki.
Ta ƙara da cewa gyare-gyaren sun haɗa da inganta mitoci da kuma farashin da ya dace da ingancin wuta, tare da ba da fifiko ga kasuwanci da masana’antu.
Tinubu ya yaba da gudunmawar masu ruwa da tsaki, yana mai cewa za a fara mataki na gaba na shirin nan ba da jimawa ba.


