Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe
Published: December 17, 2025 at 7:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC bayan murabus din Farouk Ahmad da Gbenga Komolafe

Shugaban Bola Ahmed Tinubu, ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen mutane biyu domin tantancewa da amincewa a matsayin sababbin shugabannin hukumomin kula da harkokin mai da iskar gas na ƙasa.

Nadin ya biyo bayan murabus ɗin Injiniya Farouk Ahmed daga Hukumar Kula da Bangaren Mai da Gas na ƙasa (NMDPRA), da kuma Gbenga Komolafe daga Hukumar Kula da Hakar Mai ta Ƙasa (NUPRC).

An naɗa tsoffin Shugabannin ne a shekarar 2021 a zamanin tsohon Shugaba Muhammadu Buhari, bayan kafa hukumomin ƙarƙashin Dokar Masana’antar Man Fetur (PIA).

A wasiƙar da ya aike wa Majalisar Dattawa, Shugaba Tinubu ya nemi a gaggauta tantancewa da amincewa da Oritsemeyiwa Amanorisewo Eyesan a matsayin Babbar Darakta-Janar (CEO) ta NUPRC, da kuma Injiniya Saidu Aliyu Mohammed a matsayin Babban Darakta-Janar (CEO) na NMDPRA.

Eyesan ta kammala karatun Tattalin Arziki a Jami’ar Benin, kuma ta shafe kusan shekaru 33 tana aiki a Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPC) da rassa sannan ta yi ritaya a matsayin Mataimakiyar Shugabar Sashen Upstream (2023–2024), sannan ta rike mukamin Babbar Manaja ta Tsare-tsare da Dabaru daga 2019 zuwa 2023.

A nasa bangaren, Injiniya Saidu Aliyu Mohammed, haifaffen jihar Gombe a 1957, ya kammala digiri a fannin Injiniyan Sinadarai a Jami’ar Ahmadu Bello a 1981 kuma kwanan nan an sanar da shi a matsayin Darakta mai zaman kansa a kamfanin Seplat Energy.

Ya taba rike mukaman Darakta-Janar na Matatar Mai ta Kaduna da Kamfanin Iskar Gas na Najeriya, tare da shugabancin kwamitocin gudanarwa na West African Gas Pipeline Company.

Haka kuma, ya taba zama Darakta-Janar kuma Mataimakin Shugaban Ayyuka (COO) na Sashen Gas da Wutar Lantarki, inda ya taka rawa a manyan tsare-tsaren gas na ƙasa, ciki har da Gas Masterplan, Gas Network Code, da kuma bayar da gudummawa wajen tsara dokar PIA.

Injiniya Saidu Mohammed ya kasance cikin masu jagorantar manyan ayyuka kamar fadada bututun iskar gas na Escravos–Lagos, aikin bututun Ajaokuta–Kaduna–Kano (AKK), da ayyukan Nigeria LNG.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Ministan Kudin Najeriya: Bamu Samu Kudaden Da Muke Tsammani A Wannan Shekarar Ba
Next Post: SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne

Karin Labarai Masu Alaka

Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina Najeriya
Rundunar Operation Hadinkai Sunyi Nasara Akan ISWAP Da Boko Haram Najeriya
Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya
Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet
  • Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Dusar Kankara Ta Hana Jirage Tashi A Birnin Paris Labarai
  • Rasha Ta Nuna Kudurin Cimma Zaman Lafiya Da Ukraine Amurka
  • Sabon Magajin Garin New York Zai Soke Wasu Dokoki Amurka
  • Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
  • Ƙungiyoyin Premier 17 Za Su Rasa ‘Yan Wasa 40 saboda Gasar AFCON 2025, Wasanni
  • Koriya Ta Arewa Ta Gudanar Da Gwajin Makami Mai Linzami Tsaro
  • Gwamnan Jihar Kano Ya Fice Daga Jam’iyar NNPP Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.