Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe
Published: December 17, 2025 at 7:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC bayan murabus din Farouk Ahmad da Gbenga Komolafe

Shugaban Bola Ahmed Tinubu, ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen mutane biyu domin tantancewa da amincewa a matsayin sababbin shugabannin hukumomin kula da harkokin mai da iskar gas na ƙasa.

Nadin ya biyo bayan murabus ɗin Injiniya Farouk Ahmed daga Hukumar Kula da Bangaren Mai da Gas na ƙasa (NMDPRA), da kuma Gbenga Komolafe daga Hukumar Kula da Hakar Mai ta Ƙasa (NUPRC).

An naɗa tsoffin Shugabannin ne a shekarar 2021 a zamanin tsohon Shugaba Muhammadu Buhari, bayan kafa hukumomin ƙarƙashin Dokar Masana’antar Man Fetur (PIA).

A wasiƙar da ya aike wa Majalisar Dattawa, Shugaba Tinubu ya nemi a gaggauta tantancewa da amincewa da Oritsemeyiwa Amanorisewo Eyesan a matsayin Babbar Darakta-Janar (CEO) ta NUPRC, da kuma Injiniya Saidu Aliyu Mohammed a matsayin Babban Darakta-Janar (CEO) na NMDPRA.

Eyesan ta kammala karatun Tattalin Arziki a Jami’ar Benin, kuma ta shafe kusan shekaru 33 tana aiki a Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPC) da rassa sannan ta yi ritaya a matsayin Mataimakiyar Shugabar Sashen Upstream (2023–2024), sannan ta rike mukamin Babbar Manaja ta Tsare-tsare da Dabaru daga 2019 zuwa 2023.

A nasa bangaren, Injiniya Saidu Aliyu Mohammed, haifaffen jihar Gombe a 1957, ya kammala digiri a fannin Injiniyan Sinadarai a Jami’ar Ahmadu Bello a 1981 kuma kwanan nan an sanar da shi a matsayin Darakta mai zaman kansa a kamfanin Seplat Energy.

Ya taba rike mukaman Darakta-Janar na Matatar Mai ta Kaduna da Kamfanin Iskar Gas na Najeriya, tare da shugabancin kwamitocin gudanarwa na West African Gas Pipeline Company.

Haka kuma, ya taba zama Darakta-Janar kuma Mataimakin Shugaban Ayyuka (COO) na Sashen Gas da Wutar Lantarki, inda ya taka rawa a manyan tsare-tsaren gas na ƙasa, ciki har da Gas Masterplan, Gas Network Code, da kuma bayar da gudummawa wajen tsara dokar PIA.

Injiniya Saidu Mohammed ya kasance cikin masu jagorantar manyan ayyuka kamar fadada bututun iskar gas na Escravos–Lagos, aikin bututun Ajaokuta–Kaduna–Kano (AKK), da ayyukan Nigeria LNG.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Ministan Kudin Najeriya: Bamu Samu Kudaden Da Muke Tsammani A Wannan Shekarar Ba
Next Post: SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne

Karin Labarai Masu Alaka

Dangote Ya Bukaci ICPC Ta Binciki Shugaban NMDPRA Najeriya
Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Alaka Na Cigaba Da Kamari Tsakanin Rwanda Da Barundi Labarai
  • Kauran Bauchi: Muna Nan A PDP Daram! Siyasa
  • Tinubu Ya Maye Gurbin Badaru Da Tsohon Soja Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka
  • Ambaliyar Ruwa Ya Tilastawa Dubban Jama’a Rasa Muhallensu A Morocco Afrika
  • Gobara Mafi Muni Cikin Shekaru 60 A Hong Kong Ta Hallaka Rayuka Sauran Duniya
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Yi Ma Wasu Mutane Yankan Rago A Jihar Neja Labarai
  • Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.