Shugaban Amurka Donald Trump yayi barazanar tarwatsa duk wata gada da cibiyar makamashi a Iran, abinda zai wuce gona da iri, har wasu kwararru a fannin dokokin soji suke cewa zai iya zama saba dokar yaki.
Abinda za’a duba shine ko ya kamata a kai wa wuraren hari, kuma hari ya dace da irin harin da itama Iran din ta kai, sannan kuma ko za’a iya kaucewa asarar rayukan farar hula da dama.
Barazanar da Trump yayi bata yi la’akari da irin cutarwa da za’a yiwa fararen hula ba, abinda ya sa ‘yan jam’iyyar democrat a majalisa da wasu Jami’an Majalisar Dinkin Duniya da kuma masana dokokin soji suka ce irin wadannan hare-hare zasu sabawa dokokin kasa da kasa.


