Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran
Published: April 12, 2026 at 8:48 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron yace ya zanta da shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian, ya kuma jaddada masa muhimmancin lafa rikici yayin tattaunawar tsagaita wuta a Pakistan.

Ba tabbacin ci gaba a tattaunawar sulhu

A cikin mabanbantan rahotanni da kafafen yada labarai daga jami’ain a Amurka da Iran, ya nuna cewa kasashen biyu basuyi kusa da cimma matasaya ba.

Kafin a fara tattaunawa, wani babban jami’i a Iran ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa Amurka ta yarda da zata saki kadarorin Iran da aka rike a Qatar da sauran bankunan dake wasu kasashe. Amma wani jami’in Amurka nan da nan ya musanta hakan.

Banda sakin kadarorin ta dake kasashen waje, fadar gwamnatin Tehran ta bukaci da ta mallaki ikon tafiyar da mashigin ruwa na Hormuz, da biyan diyyar yaki da kuma tsagaita wuta a yankin baki daya har da a kasar Lebanon a cewar jami’ai da kafar talabijin ta Iran.

A nasa bangaren bukatun da shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar sun sha banban, mafi karancin su yace yana son a rika gudanar da wucewa da kayayyaki ta mashigin ruwan na Hormuz daga ko ina a duniya ba tare da fuskantar kalubale ba, da kuma dakile shirin makamashin nukiliya na Iran domin a tabbatar bazata iya hada atomic bomb ba.

Isra’ila, wadda ta hadu da Amurka wajen kaiwa Iran hari a yakin da aka fara shi ranar 28 ga Watan Fabrairu, ta kuma kasance tana sakarwa ‘yan kungiyar Hezbollah da Iran ke marawa baya bama-bamai a kasar Lebanon, ta kuma ce yakin da ake a Lebanon baya cikin yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran.

Afrika, Amurka, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Amurka Da Iran Sun Tattauna A Kasar Pakistan

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Gudanar Da Zanga-Zanga Bisa Matsalar Tsaro Tsaro
Majalisa A Kasar Somaliya Ta Amince Da Sauya Tsarin Mulkin Kasar Afrika
Sakataren Kungiyar NATO Yayi Magana Da Hukumomin Kasashe Afrika
Gwamnatin Sojan Burkina Faso Ta Soke Jam’iyyun Siyasar Kasar Afrika
Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
Indiya Da Brazil Sun Kulla Yarjejeniyar Cinikayya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran
  • Amurka Da Iran Sun Tattauna A Kasar Pakistan
  • Kotu A Najeriya Ta Kame Mutane Bisa Zargin Ta’addaci
  • Shugaban Ƙasar Djibouti Ya Sake Lashe Zaben Shugaban Kasar
  • Gwamnatin Najeriya Ta Tura Mutane 386 Gidan Yari

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasashe 5 Da Ke Fama Da Matsanancin Zazzabin Cizon Sauro Rediyo
  • ‘Yan-Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Daliban St. Mary! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada Afrika
  • Zaizayar Kasa Tayi Ajalin Mutane 200 A Kasar Congo Afrika
  • Kirana Ga ‘Yan Siyasar Arewa, Su Jira Sai 2031- Akume Labarai
  • Masu Goyon Bayan Palasdinawa Sunyi Gangamin Zanga Zanga A Australia Labarai
  • Kungiyar Kwallon Mata Sun Tsallaka Iyakar Turkiyya Zuwa Iran Afrika
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Gyara Dokar Kasafin Kudi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.