Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai

Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u
Published: December 14, 2025 at 11:08 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jam’iyyar APC da Shugaba Bola Tinubu sun fara aiwatar da wata babbar dabarar siyasa domin tabbatar da nasara a zaben shugaban kasa na 2027, ta hanyar karfafa ikonsu a yankunan Kudu da Arewa ta Tsakiya.

Majiyoyi daga APC sun ce an fara shirin tun fiye da watanni biyar da suka wuce, bayan rahotannin sirri sun nuna yiwuwar barazana daga Arewa da kuma bullowar hadakar jam’iyyun adawa.

Shirin na da nufin rage tasirin adawar Arewa ta hanyar samun dunkulen kuri’u daga Kudu da Arewa ta Tsakiya.

Kungiyoyin Arewa da wasu fitattun ‘yan siyasa sun nuna rashin jin dadi da mulkin Tinubu, lamarin da ya sa APC ke kokarin karbe dukkan jihohin Kudu a 2027.

A zaben 2023, jam’iyyun adawa sun lashe jihohi da dama a Kudu da Arewa ta Tsakiya, ciki har da Lagos da Abuja.

APC ta ce tana amfani da kulla kawance, jawo hankalin manyan jiga-jigai da kuma tasirin gwamnatin tarayya domin kwato wadannan jihohi.

Jam’iyyar ta yi imanin cewa samun cikakken goyon bayan Kudu zai bai wa Tinubu gagarumar dama ta lashe zabe wa’adi na biyu.

Siyasa

Post navigation

Previous Post: Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamna Fubara: Rashin Kariya daga PDP Ne Ya Tilasta Ni Komawa APC Siyasa
Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria Siyasa
Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC Siyasa
Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ECOWAS Zata Kafa Rundunar Yaki Da Rashin Tsaro
  • Abu Mafi Daukar Hankali A Wasan Dambe Na Yau
  • Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro
  • Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro
  • Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Rundunar Tsaro Suna Cigaba Da Nasara Akan ‘Yan Ta’adda Tsaro
  • Gwamnatin Soji A Nijar Ta Hana Fitar Da Albarkatun Kasa Afrika
  • Wasu Yara 50 Sun Kubuta Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai
  • Kauran Bauchi: Muna Nan A PDP Daram! Siyasa
  • ‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.