‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
Al Ummar Garin Gwana dake Karamar Hukumar Alkaleri Jihar Bauchi Arewa maso gabas a Najeriya Suna Cigaba da Fuskanta Barazanar ‘yan Bindiga inda suke Cigaba da Kashe Mutane
Wani mazaunin Yankin Maikudi Lamido Futuk ya bayyana cewa maharan sun Kashe Mutane a Garin Digare da garin Mansur inda yawancin Mutane Suka gujewa domin tsira da Rayuwar su.

“Maikudi Lamido yace a cikin Wadanda aka kashe harda dansa wanda yake aikin jami’an sakai na vigilentee a yankin.
Yakara da cewa a Baya idan suka sace Mutane Suna Neman Kudin Fansan Anma ‘yan bindigar Suna Cigaba da sace Mutane Suna Ajeye su a wajensu a halin yanzu, ya jadda da cewa a yanzu haka Suna Cigaba da sace Kayan Abinci da Daukar dukiyoyin al’umma yayinda al’umma kuwa Suke tserewa Suna barin muhallen su domin tsira da Rayuwar su.”

Sannan “Habib Sambo Mazaunin Gwana Dake Karamar hukumar Alkaleri yace Mata da yawa Suna guduwa suna barin ‘ya’yansu a wannan yanayi da suke ciki, sun bukaci gwamnatin a dukkan matakai da kungiyoyin Bada agaji dasu Kai Musu Dauki domin Taimakon Rayuwar su.”


