Mutane na ci gaba da tserewa daga gidajen su a kauyukan da ke jihar Sokoto sakamakon barazanar da ‘yan ta’adda suke musu.
Al’ummar karamar hukumar Isa sun koka kan yadda hare-haren ‘yan ta’addar yayi tsamari, tun bayan da shugaban wata kungiyar ‘yan ta’adda ya yi barazanar hallaka mazauna kauyen Tidibali, da yake zargin sun yi musu shune wajen jami’an tsaro, idan basu bar garin ba, ranar Jumu’ar da ta gabata.
Bello Turji ya far wa Tidibali, inda ya kashe mutane 3, kuma yayi gargadin idan ya sake dawowa kowaye ya tarar zai shaki lahira, don ko kaza ba zai bari ba.
Mazauna yankin sun ce wasu daga cikin ‘yan uwan su na tserewa kasar Nijar, ta bin hanyoyi masu matukar hatsari don su tsira da rayukan su.
Mutane da dama sun tsere zuwa kasar Nijar a cewar mazauna yankin, inda wasu suka kwashe iyalan su kaf, har da iyaye. Amma akwai wadanda sukai rashin sa’a, hukumomin Nijar suka kama su suka dawo da su Nigeria.


