Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Dakarun Operation Fansan Yamma Sun Ceto Mutane 48 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Afrika
  • NDLEA Ta Kama Dan Kasuwa Da Ke Yunkurin Safarar Hodar Iblis Afrika
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika

An Shirya Taron Horas Da Matasa Gabanin Wasan Motsa Jiki 2025
Published: December 6, 2025 at 11:32 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 7, 2025

An shirya taron kara wa juna sani na kwana daya don tunkarar wasannin Motsa jiki a Jihar Bauchi.

Ma’aikatar Matasa da Wasanni na jihar Bauchi a tarayyar Najeriya,ta shirya taron bita don kara wa juna Ilimi kan wasannin Motsa jiki na Matasa karo na hudu, da zai gudana a Jihar Bauchi.

Kwamishinan Ma’aikatar Matasa da Wasanni Hon Babayo Adamu Gabarin, wadda ya samu wakilcin mai rikon Babban Sakatare a ma’aikatar Alh Abdullahi Ibrahim ya bayyana maka sudin shiya wannan taron.

Ya ce an shirya bitanne wa Jagororin Wasanni (Sport Officer) da suke kananan hukumomi ashirin dake fadin jihar Bauchi don sani ka’idoji da kuma yadda za’a ciyar da Bauchi gaba ta fanin wasannin.

Cikin bayanin sa Kwamishinan yace ya zamo dole su tabbatar da cewa sun debo ‘yan wasa na jiha banda dauko wasu a wajen jiha, ya kuma jadda aniyar gwamnati na basu goyan baya yakara da bayyana muhimmancin shirya wannan gasa shine don a samu a zakulo yara masu hazaka wa ‘yanda zasu wakilci jiha a wasannin Kasa.

Kwamishinan yace saboda maigirma Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Muhammad yayi dukkanin abunda ya dace wa bangaren Matasa da Wasanni a jiha kuma ya dukufa wajan gyara da kuma gina sabbin wajan wasanni a fadin jihar Bauchi wacce ake mata ta ke da (Mecca of Sport).

An ja hankalin mahalarta taron da su bi dokokin Gasar dan kauce wa hukunci yayin wannan wasa da za’ayi shi ranar 13 ga watan Disamba a kuma rufe 20 ga watan 10/ 2025, kwanaki bakwai kinan.

Mun samar da dukkanin kayayakin da ake bukata don ganin gasar ya tafi kamar yadda aka tsara ” in ji shi.

Kananan hukumomi ashirin ne da suke fadin jihar Bauchi zasu halarci wannan gasa inda za’ayi Wasanni kala-kala har sama da ashirin da suka shafi guje-guje tsale-tsale kokawa, to kwallon kwando, damben zamani da ma sauran wasannin irin zamani ciki harda wasannin gargaji irin su langa.

Wasannin ya kunshi bangaren Maza da Mata da ma bangaren masu bukata ta musamman wato (Para Soccer).

Manyan baki da suka halarci wannan taron sun hada da tsaffin Daraktoci a Hukumar wasanni na jihar Bauchi, da wadda ya ke kai da Shugaban Hukumar Alh Ado Amah, da wasu Jagororin gidan bangaren Mata inda dukkanin su suka bada lakca kan yadda za’a tun kari gasar cikin sauki.

Daya daga cikin mahalarta taron Abdulmalik Aminu wadda shine jami’in wasanni na karamar hukumar Bauchi, kuma Shugaban jami’ai na wasani a jiha, ya bayyana farin cikinsa da wannan taron horaswan inda yace zasuyi anfani da abunda a ka koya musu da zaran sun koma wajan aikinsu don zakulu hazikan yara da zasu fafata a gasar kuma su wakilci jiha a matakin tarayyar.

Ya kuma gode wa ma’aikatar Matasa da Wasanni na jihar Bauchi karkashin Hon Babayo Adamu Gabarin, da sukayi wannan tunani na kara wa juna sani. Yayin wannan taro an raba wa mahalarta taron takardar shaidan halartan horaswar (Certificate).

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja
Next Post: Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Arsenal Tana Ci Gaba Da Kokarin Dauko Morgan Rogers Wasanni
Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025 Wasanni
Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo Wasanni
FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Dakarun Operation Fansan Yamma Sun Ceto Mutane 48 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
  • NDLEA Ta Kama Dan Kasuwa Da Ke Yunkurin Safarar Hodar Iblis
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
  • Kamfanin Hakar Ma’adanai Na Kasar Kanada Ya Cigaban Da Aikinsa Labarai
  • Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Musulmai Murnar Sallah, Tare Da Kira Zuwa Ga Kishin Kasa Afrika
  • Kasashen Yankin Gulf Sun Bada Sanarwa Afrika
  • Amurka Zata Bawa Ukraine Tsaro Na Musamman Amurka
  • Iran Tace Farisa Zata Kai Hari Kan Mayakan Amurka Amurka
  • Thailand Da Cambodia Sun Fara Tattauunawa Kan Batun Tsagaita Wuta Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.