Rundunar sojojin kasar Bangladesh ta ce an kashe sojojinta su akalla 6 masu aikin kiyaye zaman lafiya, kuma aka raunata wasu guda 8 a harin da aka kai kan wani sansanin ‘yan kiyaye zaman lafiya na MDD a Abyei a kasar Sudan.
A cikin wata sanarwar da ta bada, rundunar ta ce har yanzu ana ci gaba da gwabza fada da ‘yan ta’adda a wurin, kuma hukumomi suna kokarin neman yadda zasu kula da wadanda suka ji rauni ko kwashe su daga wurin.
Bangladesh tana daya daga cikin kasashen da suka fi bayar da gudumawar sojoji ga ayyukan kiyaye zaman lafiya na MDD a fadin duniya, kuma an jima da girka sojojinta a garin na Abyei dake wani yankin da ake takaddamar mallakarsa a tsakanin Sudan da Sudan ta Kudu.


