Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco
Published: December 15, 2025 at 9:14 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sanyi mai tsanani ya kase wasu bakin haure ‘yan Afirka a kusa da bakin iyakar Morocco da Aljeriya.

Kungiyoyin kare hakkin bil Adama a kasar dake Afirka ta Arewa sun bayyana wannan a matsayin babban abin damuwa kuma abinda ya keta ‘yancin zirga-zirgar murtane.

Wata gamayyar kungiyoyin kare hakkin bil Adama a kasar Morocco, ta ce an gano gawarwakin maza 7 da mata biyu a yankin Ras Afour mai tsaunuka, inda sanyin hunturu yake yayi tsanani sosai.

Kungiyar ta ce wadannan bakin haure ‘yan gudun hijira sun mutu a sanadiyyar sanyi mai tsanani wanda jikinsu dake gajiye ba zai iya dauka ba.

An ce daya daga cikin ‘yan gudun hijirar dan kasar Guinea ne.

A duk shekara, dubban ‘yan Afirka dake kwadayin zuwa kasashen turai su na bi ta cikin hamadar Sahara zuwa kasashen Afirka ta yamma daga inda suke fatan tsallakawa zuwa turai, amma irin wannan balaguro yana da tsananin hadari, kuma daruruwa suna mutuwa ba tare da sun kai inda suke son zuwa ba.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO
Next Post: Gwamnatin Tarayya Na Kokarin Hana Demokraɗiyya A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Koriya Ta Arewa Ya Gabatar Da Gwajin Makami Mai Linzami Afrika
An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
Togo Ta Kama Tsohon Shugaban Kasar Burkina Faso Saboda Kitsa Juyin Mulki Afrika
Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
Prime Ministar Italiya Ta Ziyarci Saudi Arabia Afrika
‘Yan Sanda A Finland Sun Kwace Jirgin Ruwan Kasar Rasha Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Da Tarayyar Turai Sun Fidda Sanarwa Afrika
  • Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Shugaba Trump Tana Cigaba Da Janye Jakadunta Zuwa Gida Amurka
  • Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Yayi Ajalin ‘Yan Ghana 50 Afrika
  • Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba Labarai
  • Hukumar EFCC Ta Kama Dan Kasuwa A Kamaru Afrika
  • Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.