Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Gwamnatin Kebbi Ta Samu Tankokin Yaki
Published: December 16, 2025 at 10:22 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ’Yan Sandan Najeriya ta miƙa motocin yaki masu sulke guda 13 ga Gwamnatin Jihar Kebbi, domin ƙarfafa yaƙi da ’yan bindiga da sauran laifuka a jihar.

An miƙa motocin ne a Gidan Gwamnati da ke Birnin Kebbi, inda Kwamishinan ’Yan Sanda na jihar, CP Bello Sani, ya ce an turo su ne daga hedikwatar rundunar a Abuja bisa umarnin Babban Sufeton ’Yan Sanda.

A martaninsa, Gwamna Nasir Idris ya yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu da shugabancin rundunar ’yan sanda, yana mai cewa motocin za a tura su zuwa muhimman wuraren da ke fama da matsalolin tsaro, musamman a kan iyakokin Zamfara da Neja, domin bai wa manoma damar yin girbi cikin aminci.

Gwamnan ya jaddada cewa, tsaro ne ginshiƙin ci gaba, tare da tabbatar da ci gaba da bai wa hukumomin tsaro cikakken goyon baya domin tabbatar da zaman lafiya a Jihar Kebbi.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro
Next Post: Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71

Karin Labarai Masu Alaka

Rundunar ‘Yan Sandan Kebbi Ta Dakile Yunkurin Garkuwa Da Mutune, Ta Kama Masu Laifi Afrika
Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Filato Ta Gurfanar Da Maharan Rukuba A Kotu Afrika
Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
Sanarwar MDD Ya Nuna Aniyar Mayakan RSF Na Kisan Kare Dangi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Afrika
  • Gwamnatin Jihar Neja Ta Soke Lasisin Mallakar Wasu Manyan Filaye A Jihar Labarai
  • An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade Wasanni
  • ‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
  • Dan Wasan Gaba Na Manchester United, Zirkzee Ya Amince Da Komawa Juventus Ko Napoli Wasanni
  • Angano Gawar Wani Dan Myanmar A Arewacin New York Afrika
  • NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya
  • Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.