Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Karo Na Biyu Cikin Kwanaki 29 An Samu Gobara A Kasuwar Katako
Published: December 16, 2025 at 11:04 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 16, 2025

Wakilin GTA Hausa “Amurka Ke Magana” a Gombe, Aliyu Bala Gerengi, ya rawaito cewa gobarar ta tashi ne a daren ranar Litinin, inda ake zargin matsalar lantarki ce ta haddasa ta, lamarin da ya jawo konewar shaguna da dama da kuma kayayyaki da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

Wannan iftila’i ya faru ne kwanaki 29 kacal bayan da wani ɓangare na kasuwar, musamman sashen tsofaffin ƙarafa da soso (scrap da metal), ya ƙone a ranar 17 ga Nuwamba, inda gobarar ta lalata shaguna fiye da 30 tare da dukiyoyi da aka kiyasta darajarsu ta haura naira miliyan 500.

A daren Litinin ɗin, wani ɓangare na kasuwar ya sake kamawa da wuta, abin da ya ƙara tsananta asarar da ’yan kasuwar suka tafka, musamman waɗanda itace kawai hanyar cin abincin su.

Amma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ba da umarnin gudanar da bincike kan gobarar da ta tashi a kasuwar katako a jihar, wacce ta ƙone shaguna da kayayyaki masu yawa, lamarin da ya janyo asarar dukiya mai yawa ga ‘yan kasuwa da dama.

Gwamnan Inuwa Yahaya, ya bayyana alhini da jimami matuƙa bisa faruwar wannan lamarin.

A cikin wata sanarwa da Darakta-janar na harkokin yaɗa labarai na gwamnatin jihar, Ismaila Uba Misilli, ya fitar, gwamnan ya bayyana lamarin a matsayin babban rashi da juyayi ga al’ummar da abin ya shafa, tare da miƙa saƙon jaje ga dukkan ‘yan kasuwa da masu shagunan da gobarar ta rutsa da su.

Sanarwar ta ce “Gwamna Inuwa ya tabbatar wa waɗanda abin ya shafa cewa gwamnatin jihar tana tare da su a wannan lokaci na radadi, inda ya umarci hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar wato (SEMA) da sauran hukumomi masu alaƙa da su da su hanzarta bincike kan musabbabin gobarar, tare da kai tallafi da agajin gaggawa ga waɗanda abin ya shafa.

Gwamnan ya kuma jaddada ƙudirin gwamnatinsa na kafa wata cibiyar kwana-kwana ta zamani mai kayan aiki da ƙwarewa domin ƙarfafa kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71
Next Post: Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi

Karin Labarai Masu Alaka

Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia Afrika
Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Don Neman Zaman Lafiya Labarai
Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
Bankin Duniya Zaibawa Kasar Mozambique Lamunin Dala Bilyan Shida Labarai
Hukumar Zaben Najeriya Ta Sanar Da Ranar Zaben Shugaban Kasa Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Anyi Girgizar Kasa Mai Karfi A Kasar Mexico Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Suvr Jahun: Ya Kamata Obasanjo Ya Bar Al’umar Ƙasa Su Fito Da Wadda Suke So 2027 Najeriya
  • Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika
  • Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
  • Akwai Shakku Akan Sanin Wacce Kungiyar Kwallon Kaface Zata Lashe Gasar Kofin Afirka Da Akeyi A Morocco Nishadi
  • An Zargi Babban Mai Gabatar Da Kara A Kotun Duniya Ta ICC Afrika
  • Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.