Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Karo Na Biyu Cikin Kwanaki 29 An Samu Gobara A Kasuwar Katako
Published: December 16, 2025 at 11:04 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 16, 2025

Wakilin GTA Hausa “Amurka Ke Magana” a Gombe, Aliyu Bala Gerengi, ya rawaito cewa gobarar ta tashi ne a daren ranar Litinin, inda ake zargin matsalar lantarki ce ta haddasa ta, lamarin da ya jawo konewar shaguna da dama da kuma kayayyaki da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

Wannan iftila’i ya faru ne kwanaki 29 kacal bayan da wani ɓangare na kasuwar, musamman sashen tsofaffin ƙarafa da soso (scrap da metal), ya ƙone a ranar 17 ga Nuwamba, inda gobarar ta lalata shaguna fiye da 30 tare da dukiyoyi da aka kiyasta darajarsu ta haura naira miliyan 500.

A daren Litinin ɗin, wani ɓangare na kasuwar ya sake kamawa da wuta, abin da ya ƙara tsananta asarar da ’yan kasuwar suka tafka, musamman waɗanda itace kawai hanyar cin abincin su.

Amma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ba da umarnin gudanar da bincike kan gobarar da ta tashi a kasuwar katako a jihar, wacce ta ƙone shaguna da kayayyaki masu yawa, lamarin da ya janyo asarar dukiya mai yawa ga ‘yan kasuwa da dama.

Gwamnan Inuwa Yahaya, ya bayyana alhini da jimami matuƙa bisa faruwar wannan lamarin.

A cikin wata sanarwa da Darakta-janar na harkokin yaɗa labarai na gwamnatin jihar, Ismaila Uba Misilli, ya fitar, gwamnan ya bayyana lamarin a matsayin babban rashi da juyayi ga al’ummar da abin ya shafa, tare da miƙa saƙon jaje ga dukkan ‘yan kasuwa da masu shagunan da gobarar ta rutsa da su.

Sanarwar ta ce “Gwamna Inuwa ya tabbatar wa waɗanda abin ya shafa cewa gwamnatin jihar tana tare da su a wannan lokaci na radadi, inda ya umarci hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar wato (SEMA) da sauran hukumomi masu alaƙa da su da su hanzarta bincike kan musabbabin gobarar, tare da kai tallafi da agajin gaggawa ga waɗanda abin ya shafa.

Gwamnan ya kuma jaddada ƙudirin gwamnatinsa na kafa wata cibiyar kwana-kwana ta zamani mai kayan aiki da ƙwarewa domin ƙarfafa kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71
Next Post: Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar Zabe A Kasar Honduras Ta Sanar Da Nasry Asfura A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Shugaban Ƙasa Afrika
Tattalin Arzikin Kasar Uganda Zai Bunkasa A Wannan Shekarar Labarai
Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara Labarai
Gwamnatin Najeriya Tana Saka Ido Akan Matsalolin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Shugaban Kasar Uganda Yana Kokarin Mayar Da Mulkin Kasar Na Gado Labarai
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Jama’ar Arewa Maso Gabas Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hari Akan Wata Mashaya Ya Rutsa Da Mutane 9 A Afirka Ta Kudu Afrika
  • Akwai Yiwuwar Shugaban Ƙasar Afirka Ta Tsakiya Touadera Yasamu Nasara A Karo Na Uku Afrika
  • Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Trump: Washington Zatayi Cinikayya Da Indiya Amurka
  • ‘Yan Tawayen Kasar Kwango Ne Suka Kai Hari Filin Jirgin Saman Kisangani Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Bukaci Jakadan Israela Ya Fice Daga Kasar Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s Tsaro
  • Wasu Lauyoyi Sunyi Murabus Yayin Gudanar Da Wata Shari’a A Kasar Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.