Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Karo Na Biyu Cikin Kwanaki 29 An Samu Gobara A Kasuwar Katako
Published: December 16, 2025 at 11:04 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 16, 2025

Wakilin GTA Hausa “Amurka Ke Magana” a Gombe, Aliyu Bala Gerengi, ya rawaito cewa gobarar ta tashi ne a daren ranar Litinin, inda ake zargin matsalar lantarki ce ta haddasa ta, lamarin da ya jawo konewar shaguna da dama da kuma kayayyaki da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

Wannan iftila’i ya faru ne kwanaki 29 kacal bayan da wani ɓangare na kasuwar, musamman sashen tsofaffin ƙarafa da soso (scrap da metal), ya ƙone a ranar 17 ga Nuwamba, inda gobarar ta lalata shaguna fiye da 30 tare da dukiyoyi da aka kiyasta darajarsu ta haura naira miliyan 500.

A daren Litinin ɗin, wani ɓangare na kasuwar ya sake kamawa da wuta, abin da ya ƙara tsananta asarar da ’yan kasuwar suka tafka, musamman waɗanda itace kawai hanyar cin abincin su.

Amma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ba da umarnin gudanar da bincike kan gobarar da ta tashi a kasuwar katako a jihar, wacce ta ƙone shaguna da kayayyaki masu yawa, lamarin da ya janyo asarar dukiya mai yawa ga ‘yan kasuwa da dama.

Gwamnan Inuwa Yahaya, ya bayyana alhini da jimami matuƙa bisa faruwar wannan lamarin.

A cikin wata sanarwa da Darakta-janar na harkokin yaɗa labarai na gwamnatin jihar, Ismaila Uba Misilli, ya fitar, gwamnan ya bayyana lamarin a matsayin babban rashi da juyayi ga al’ummar da abin ya shafa, tare da miƙa saƙon jaje ga dukkan ‘yan kasuwa da masu shagunan da gobarar ta rutsa da su.

Sanarwar ta ce “Gwamna Inuwa ya tabbatar wa waɗanda abin ya shafa cewa gwamnatin jihar tana tare da su a wannan lokaci na radadi, inda ya umarci hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar wato (SEMA) da sauran hukumomi masu alaƙa da su da su hanzarta bincike kan musabbabin gobarar, tare da kai tallafi da agajin gaggawa ga waɗanda abin ya shafa.

Gwamnan ya kuma jaddada ƙudirin gwamnatinsa na kafa wata cibiyar kwana-kwana ta zamani mai kayan aiki da ƙwarewa domin ƙarfafa kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71
Next Post: Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi

Karin Labarai Masu Alaka

An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash Labarai
Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC Labarai
Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
Shugaban Kasar Tunisiya Ya Tsawaita Dokar Da Baci A Kasar Labarai
‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi Labarai
Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Amurka Zata Bawa Ukraine Tsaro Na Musamman Amurka
  • Hukumar ICPC Ta Kwato Makudan Kudade Rediyo
  • Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi Afrika
  • Bana Ba Harka Ga ‘Yan-Wasan Kwallon Kafar Najeriya Wasanni
  • Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango Labarai
  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna Labarai
  • Gwamna Fubara: Rashin Kariya daga PDP Ne Ya Tilasta Ni Komawa APC Siyasa
  • Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.