Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya
Published: December 17, 2025 at 5:13 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gabannin zanga-zangar ƙasa baki ɗaya da Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) za ta gudanar a yau laraba, rundunar ‘yan sanda ta tura jami’an tsaro na musamman domin tabbatar da zaman lafiya da hana tashin hankali.

NLC ta jaddada cewa ba za ta janye zanga-zangar ba, wadda aka shirya sakamakon tabarbarewar tsaro, tsadar rayuwa, da sauran matsalolin ma’aikata.

Kakakin ƙungiyar, Benson Upah, ya yi gargaɗi cewa duk wani yunƙurin kawo cikas ko cutar da ko da mutum ɗaya zai iya haifar da yajin aikin ƙasa baki ɗaya na dindindin.

Ƙungiyar ta ce ta samu bayanan sirri na yiwuwar shigar ‘yan daba ko ‘yan siyasar haya cikin zanga-zangar, tare da kiran mambobinta da al’umma su kasance cikin lumana da haɗin kai.

NLC ta bayyana zanga-zangar a matsayin matakin ‘yan ƙasa gaba ɗaya na neman ingattaccen tsaro da gyaran shugabanci, tana mai kira ga ‘yan sanda su kare ‘yancin jama’a na taruwa don bayyana koke-koken su bisa dokar kasa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri
Next Post: Lawal, Filin Wasa Na Rashidi Yekini Ko Turai Iyaka

Karin Labarai Masu Alaka

Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba Labarai
An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai
Hukumar Zabe Ta Saukaka Gudanar Da Rijistar Katin Zabe A Najeriya Labarai
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wani Jirgin Sama Ya Karya Dokar Hana Zirga Zirga Amurka
  • Motsepe, Daga 2028 AFCON Zata Sauya Daga Shekaru Biyu Zuwa Hudu Wasanni
  • Iran Da Amurka Zasu Kulla Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
  • Sama da mutane dubu 500 ne yanbindiga suka kora daga gidajensu a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
  • Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara Labarai
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.