Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Wasan Dambe Ya Dau Sabon Salo A Jihar Inugu
Published: December 19, 2025 at 2:56 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Al’ummar Arewa a Jihar Inugu na ci gaba da yin sam-barka tare da bayyana farin ciki da bude sabon gidan damben gargajiya da aka yi a Inugu babban birnin jihar bayan shafe shekaru da wasan ya dauke.

Mai gidan damben Cif Emeka Nnolim, wani dan kabilar Igbo ya ce, “Wannan hanya ce ta hada kawunan kabilu daban-daban na Najeriya don karfafa zumunci ta hanyar raya wasan dambe a tsakanin matasan Arewa da ke wannan jihar da wadanda suke nesa. Wannan matakin farko ne na bunkasa wasannin gargajiya a Jihar Inugu don mayar da jihar cibiyar wasannin gargajiya a Najeriya.”

Bayan kammala bude filin wasan, shugaban al’ummar Arewa a jihar da kuma babban mai taimaka wa gwamnan Jihar Inugu kan ayyuka na musamman, Alhaji Abubakar Yusuf Sambo ya tofa albarkacin bakinsa kan dawowar wasan dambe a jihar.

“Na yi farin ciki da ganin cewa da duk da cewa muna kudancin Najeriya muna tuna abin da aka san Arewa da shi watau wasan dambe. Wasa ne na hada zumunci, kuma duk inda ake irin wannan zamu bada goyon baya,” inji Alhaji Yusuf Sambo.

A cewar wani dan dambe dan asalin garin Hadejia na Jihar Jigawa mai suna Adamu wanda aka fi sani da Shagon Baturiya, “Wasa ya yi dadi yadda ake so. Sabon gidan dambe da aka bude anan Inugu ya yi kyau. Na yi farin ciki kuwa,” a yayin da wani shahararren dan wasa Badaman Bauchi, shi ma cike da farin ciki, ya mika goron gayyata zuwa daukacin ‘yan wasa da cewa:

“Filin sabon gidan wasan dambe da aka bude a Inugu ba laifi. Toh domin haka, muna kira ga sauran ‘yan wasa da suke nesa da su zo. Muna gayyatar kowa da kowa su zo.”

An bude gidan damben ne unguwar Emene wacce take cikin birnin Inugun, inda matasan Arewa sun fara tururuwa don nishadantar da kansu da take taken ‘yan wasa da kide-kiden gargajiya masu faranta ran gaske.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Sanda Sunce Mutum Daya Ne Yakai Hare-Haren Jami’ar Brown Da Kuma Na MIT Boston
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kuɗin 2026

Karin Labarai Masu Alaka

An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade Wasanni
Yan Fashi Sun Shiga Gidan Alex Iwobi A Ingila Wasanni
Hawan Sallah A Jihar Katsina Afrika
Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni
Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni
Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Umarci Janye ‘Yan Sanda Masu Gadin Ministoci Tsaro
  • Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane Tsaro
  • Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
  • Kasar Morocco Ta Kwashe ‘Yan Kasar Daga Sassan Ambaliyar Ruwa Afrika
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi Labarai
  • Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.