Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade
Published: December 21, 2025 at 8:15 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 21, 2025

Tuhume-tuhumen cin zarafi yasa Molde FK ta dakatar da Daniel dan Najeriya.

Dan wasan tsakiya na kwallon kafa ta Najeriya mai tashe Daniel Daga, yana fuskantar shari’a bayan ana tuhume shi da laifin cin zarafin wa ta mata ba tare da izini ba a kasar Norway.

Kungiyarsa ta Molde FK, ta tabbatar da wannan lamari, wanda ya haifar da cece kuce a tsakanin ‘yan wasan Eliteserien da kuma ‘yan wasan kwallon kafa ta Najeriya, a wata sanarwa da ta aka fitar a ranar Juma’a.

Matashin dan wasan mai shekaru 18, wanda kwanan nan ya koma buga kwallon kafa a Turai, an dakatar da shi daga dukkan ayyukan kungiyar, da suka hada da notsa jiki da wasannin gasa, yayin da ake ci gaba da shari’ar.

A cewar mai gabatar da kara, tuhume-tuhumen sun samo asali ne daga wani lamari da ya faru a lokacin kakar wasa ta farko a Norway.

Duk da cewar ba’a sanar da cikakken bayanin abun da ya faru ba, don kare bangarorin da abin ya shafa, Kotun Gundumar Nordmøre da Romsdal ta tsara zaman sauraren karar a watan Maris na 2026.

An ruwaito cewa dan wasan ya kasance mai bada hadin kai a duk lokacin binciken farko, yana halartar da amsa duk tambayoyin da ‘yan sanda suka yi masa.

Duk da cewa ya dawo Najeriya tun daga lokacin, ana sa ran zai koma Norway don fuskantar shari’ar a bazara mai zuwa.

Molde FK, ɗaya daga cikin fitattun ƙungiyoyi ne a Norway, ta ɗauki mataki mai ƙarfi kan wannan lamarin.

Shugaban ƙungiyar Odd Ivar Moen ya jaddada muhimmancin tuhumar yayin da ya amince da wahalar da lamarin ke haifarwa ga duk masu ruwa da tsaki a ƙungiyar.

“Wannan lamari ne mai mahimmanci, kuma muna ɗaukar tuhumar da muhimmanci,” in ji Moen.

“Irin waɗannan shari’o’in suna da matuƙar wahala ga duk wanda abin ya shafa.

Abin da ya fi muhimmanci shi ne mu yi aiki da gaskiya da kuma tabbatar da adalci da girmama dukkan ɓangarorin.

Ƙungiyar ta kuma ɗauki matakin tuntuɓar lauyoyin mai ƙara, tana mai amincewa da “nauyin na sirri” da shari’ar ta ɗora wa wanda abin ya shafa.

Duk da tuhumar da ake yi masa a hukumance, wadda ya ke wakiltar Daniel Daga a shara’ance ya tabbatar da cewa ba shi da laifi.

Lauyansa, Astrid Bolstad, ya tabbatar da cewa yayin faruwar lamarin jima’in ɗan wasan tsakiya ya tabbatar da cewa anyi shi bisa amince duk kanin su gaba ɗaya. Babu wata shaida ko zargin tashin hankali ko barazana da aka samu a lokacin

Daniel Daga ya je ƙungiyar ta Molde kafin kakar wasa ta 2025 a matsayin ɗaya daga cikin ‘yan wasan tsakiya masu tasowa a Afirka.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Hukumar ICPC Ta Gayyaci Dangote
Next Post: An Sako Ɗaliban Makaranta 130 Da Aka Sace A Jihar Neja 

Karin Labarai Masu Alaka

CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Lawal, Filin Wasa Na Rashidi Yekini Ko Turai Iyaka Wasanni
‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke Wasanni
CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Sanda Sun Kama Mutane Takwas Da Ake Zargi Da Siyar Da Tikitin AFCON Ba Bisa Ka’ida Ba Wasanni
Gasar Cin Kofin Nahiyar Afrika A Wannan Makon Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Amurka Zata Saidawa Saudiyya Da Jirgin Yaki Samfurin F35 Labarai
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura Labarai
  • Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Abun Da Kuke Buƙatar Sani Game Da Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka 2025 Wasanni
  • Ukraine Tana Cigaba Da Tattaunawa Da Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Kasar Amurka
  • Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya Afrika
  • Sanyi Mai Tsanani Da Dusar Kankara Ya Tsaida Al’amura A Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.