Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Majalisar Tarayya Ta Amince Da Gyara Dokar Kasafin Kudi
Published: December 24, 2025 at 7:57 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

A karon farko a tarihin Najeriya, Majalisar Dokokin Kasa ta amince wa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu yin aiki da kasafin kudin shekara 2024 da na 2025 har zuwa watan Maris na shekara 2026 mai zuwa.

Wakiliyar GTA Hausa Medina Dauda ta hada mana rahoto kan dalilan da ya sa Majalisar ta aiwatar da wannan aiki, Majalisar Dattawa da ta Wakilai sun amince da gyara kudurin dokar kasafin kudin shekara 2024 da ta 2025 inda aka dunkule kashi 70 na kudaden manyan aiyukan wadannan shekaru har zuwa watan Maris na shekara 2026 inda ake fatan kammala dukkan aiyukan a cikin lokaci kana a fara aiki da kasafin kudin shekara 2026 daga watan Afrilu.

Yan Majalisar sun goyi bayan kudurin wanda aka karanta kuma aka zartar da shi ta hanyar karatu na farko da na biyu da na uku a zama daya kamar yadda Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi na Majalisar Dattawa Sanata Solomon Adeola Olamilekan ya baiyana mana bayan sun kammala zaman a jiya talata.

Olamilekan ya ce ana bukatar karin lokaci don baiwa Gwamnatin Taraiyya damar Kammala wasu aiyuka da ake ci gaba da yi a karkashin Kasafin kudin shekara 2025.

Olamilekan ya ce an yi wannan tsawaitawan ne saboda Najeriya za ta cigaba da gudanar da kasafin kudi guda daya rak daga watan Afrilun badi don inganta amfani da kudaden da aka ware da kuma ba da damar kammala muhimman aiyukan samar da ababen more rayuwa.

A bangaren Majalisar Wakilai kuma Dan Majalisa Daga Jihar Jigawa Abubakar Hassan Fulata yayi bayanin dalilin da ya sa Majalisa ta dauki wannan mataki na tsawaita Kasafin Kudin shekra 2924 da na 2025 din cikin gaggawa Majalisa ta tafi hutun karshen shekara sai ranan 27 ga watan Janairu na shekara 2026 za su dawo bakin aiki.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji
Next Post: Anyi Rashin Mutane Da Yawa Yayinda Bom Ya Fashe Ana Sallar Magariba Maiduguri

Karin Labarai Masu Alaka

Rasha Ta Yiwa Amurka Tayin Daina Bada Bayanan Sirri Afrika
Fafaroma Leo Yayi Allah Wadai Bisa Karuwar Yake Yaken Gabas Ta Tsakiya Amurka
Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yaki Da Akeyi Tsakanin Isra’ila Da Amurka Afrika
Dusar Kankara Ta Hana Jirage Tashi A Birnin Paris Labarai
Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Kashe Mayakan Sakai 67 A Pakistan Sauran Duniya
  • EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Afrika
  • Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara Labarai
  • Harin ‘Yan Daba Ya Hallaka Mutane 70 A Kasar Haiti Labarai
  • Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.