Dan wasan dambe na kasar Birtaniya, Anthony Joshua ya yi hatsarin mota a jihar Ogun da ke Nigeria, hatsarin ya yi sanadiyar rayukan mutane biyu, a cewar ‘yan sanda ranar Litinin.
‘Yan sandan na jihar Ogun sun ce motar su Anthony Joshua ta yi karo ne da wata motar, kuma An kai shi asibiti, inda suka kara da cewa suna gudanar da bincike kan dalilin faruwar hatsarin.
Hukumar kiyaye hadura ta kasa ta ce mutane biyar ne hatsarin ya rutsa da su a hanyar Lagos-zuwa Ibadan, inda Joshua ya samu raunuka kadan, mutum biyu suka mutu, wasu biyu kuma ba su samu rauni ko kadan ba.
Hukumar ta ce, farkon bincike ya nuna motar da take dauke da Mr. Joshua tana zura gudu ne sai kan motar ya kwace, yayin da take kokarin wuce wata mota, da tayi karo da wata gingimari da ke ajiye a gefen titi.
Anthony Joshua, wanda ya kasance iyayen sa ‘yan Nigeria ne da Birtaniya, ya yi makarantar kwana ne a garin Ikenne, wanda ya ke mil 53 daga inda hatsarin ya faru, kafin daga bisani ya koma Birtaniya yana da shekara 12.


