Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela
Published: January 3, 2026 at 8:53 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 3, 2026

Game da Hambarar da Mulkin Shugaban Kasar Venezuela Hukumomin duniya kuma, sunce “Wannnnan matakin ya kasance misali mai hadari, kan yadda za’a gudanar da al’amura nan gaba” inji kakakin sakataren MDD Antonio Gutierrez, ya ci gaba da cewa, sakataren na MDD yana jaddada muhimancin dukkan kasashen duniya su su mutunta dokokin kasa da kasa, ciki harda sharudda da dokokin MDD.

Mr. Gutierrez inji mai magana da yawunsa, yana nuna matukar damuwa cewa anan dai ba’a mutunta dokokin kasa da kasa ba.”

A nata bangaren Jamus ta bakin ma’aikatar harkokin wajen kasar tace, “Muna kira ga duk wadanda wannan lamari ya shafa, su gujewa ruruta wannan yanayi, kuma su nemi hanyoyin hannyoyin warware wannan batu ta fuskar siyasa,” Ta kara da cewa, Venezuela tana bukatar ko ta cancanci zaman lafiya, da tafarkin demokuradiyya nan gaba.”

China a nata bangaren, ma’aikatar harkokin wajen kasar tace, “Sin ta kadu, kuma tayi Allah wadai da kakkausar lafazi, amfani da karfin soja kan kasa mai ‘yanci, da kuma amfani da karfin soja kan shugaban kasa.”

Shi kuma da yake magana kan wannan lamari, ministan harkokin wajen Faransa yace, “matakin soja da ya kai ga kama shugaba Maduro, ya kaucewa amfani da karfi kamar yadda yake a dokokin kasa da kasa itama faransa ta sake jaddada cewa ba za’a samu zaman lafiya mai dorewa ba, idan aka tilasta shi daga ketare, Faransa tace ‘yan kasa ne kadai za su iya shata makomar su.

Da take magana kan wannan batu, ma’aikatar harkokin wajen Rasha tace, “A safiyar nan, Amurka ta nuna fin karfi ta amfani da karfin soja kan kasar Venezuela, wannan abun damuwa ne matuka, kuma abun Allah wadai ne.

Afirka ta kudu ta bakin ma’aikatar harkokin wajen kasar, ta bukaci kwamitin sulhu na MDD, yayi zaman gaggawa domin duba wannan lamari.

A kasashe dake Latin Amurka ra’ayoyi shugabannin kasashen sun sha ban ban, wasu suna Allah wadai da matakin, wasu kuma suna san barka.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela
Next Post: Jagoran Kasar Iran Yace Basa Bukatar Tallafin Kasar Amurka

Karin Labarai Masu Alaka

Anyi Sallar Rokon Ruwa A Saudiya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Anyi Girgizar Kasa Mai Karfi A Kasar Mexico Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Gombe Ta Dauki Sabbin Matakan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Da Amurka Zasu Kulla Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
  • Hamas Ta Kwance Damara Afrika
  • Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
  • ‘Yan Kasar Venuzuela Zasu Fara Komawa Gida Amurka
  • Fafaroma Leo Yayi Allah Wadai Bisa Karuwar Yake Yaken Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Gaddafi A Gidansa Dake Kasar Libya Afrika
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Gabatar Da Kudi Fiye Da Naira Triliyan 58 A Matsayin Kasafin 2026 Najeriya
  • Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.