Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela
Published: January 3, 2026 at 8:53 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 3, 2026

Game da Hambarar da Mulkin Shugaban Kasar Venezuela Hukumomin duniya kuma, sunce “Wannnnan matakin ya kasance misali mai hadari, kan yadda za’a gudanar da al’amura nan gaba” inji kakakin sakataren MDD Antonio Gutierrez, ya ci gaba da cewa, sakataren na MDD yana jaddada muhimancin dukkan kasashen duniya su su mutunta dokokin kasa da kasa, ciki harda sharudda da dokokin MDD.

Mr. Gutierrez inji mai magana da yawunsa, yana nuna matukar damuwa cewa anan dai ba’a mutunta dokokin kasa da kasa ba.”

A nata bangaren Jamus ta bakin ma’aikatar harkokin wajen kasar tace, “Muna kira ga duk wadanda wannan lamari ya shafa, su gujewa ruruta wannan yanayi, kuma su nemi hanyoyin hannyoyin warware wannan batu ta fuskar siyasa,” Ta kara da cewa, Venezuela tana bukatar ko ta cancanci zaman lafiya, da tafarkin demokuradiyya nan gaba.”

China a nata bangaren, ma’aikatar harkokin wajen kasar tace, “Sin ta kadu, kuma tayi Allah wadai da kakkausar lafazi, amfani da karfin soja kan kasa mai ‘yanci, da kuma amfani da karfin soja kan shugaban kasa.”

Shi kuma da yake magana kan wannan lamari, ministan harkokin wajen Faransa yace, “matakin soja da ya kai ga kama shugaba Maduro, ya kaucewa amfani da karfi kamar yadda yake a dokokin kasa da kasa itama faransa ta sake jaddada cewa ba za’a samu zaman lafiya mai dorewa ba, idan aka tilasta shi daga ketare, Faransa tace ‘yan kasa ne kadai za su iya shata makomar su.

Da take magana kan wannan batu, ma’aikatar harkokin wajen Rasha tace, “A safiyar nan, Amurka ta nuna fin karfi ta amfani da karfin soja kan kasar Venezuela, wannan abun damuwa ne matuka, kuma abun Allah wadai ne.

Afirka ta kudu ta bakin ma’aikatar harkokin wajen kasar, ta bukaci kwamitin sulhu na MDD, yayi zaman gaggawa domin duba wannan lamari.

A kasashe dake Latin Amurka ra’ayoyi shugabannin kasashen sun sha ban ban, wasu suna Allah wadai da matakin, wasu kuma suna san barka.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela
Next Post: Jagoran Kasar Iran Yace Basa Bukatar Tallafin Kasar Amurka

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026 Shirye-Shirye
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
  • Kudin Man Fetur Ya Karu Da Kashi 10 Cikin 100 Afrika
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Shugaban Amurka Donald Trump Yace Bai Taba Shiga Jirgin Jeffrey Epstein Ba Labarai
  • Kasashen Yankin Gulf Sun Bukaci Amurka Takawo Karshen Iran Afrika
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.