Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki
Published: November 17, 2025 at 6:34 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Da farko a karshen makon jiya ne babbar jam’iyyar adawa a Najeriya PDP ta gudanar da taronta na kasa a birnin Badun, babban birnin jihar Oyo. inda ta zabi sabbbin shugabanni. Lauya Kabiru Tanimu Turaki, shine aka zaba sabon shugaban jam’iyyar. Aka kuma zabi Taofeek Arapaja, a matsayin sakataren jam’iyya. Babban taron ya kuma kori wasu jiga-jigan jam’iyyar da suka hada da Ministan raya birnin Tarayya Abuja Nyesom Wike da wadansu, kan zargin suna yiwa jam’iyyar zagon kasa.

Don samun haske akan wannan dambarwar, abokin aikin mu Yusuf Aliyu Harande ya tattauna da wani masanin siyasa kuma lauya mai zaman kanshi.

“Akwai bukatar jam’iyyu a Najeriya su dinga mutunta hukunce-hukuncen Kotuna, ba don komai ba kuwa sai don mutunta doka da oda daga mahukunta. Rashin mutunta hukuncin kotu da jam’iyar PDP ta yi zai iya jefa ta cikin mawuyacin hali.” A cewar Lauya Bala Usman, wani lauya mai zaman kanshi a Abuja.

Sau da yawa idan kaga ana takaddama, to abu da yafi kamata shine a garzaya kotu, don magance matsalar, kamar yadda Alh. Sule Lamido, tsohon gwamnan jihar Jigawa, yayi na garzayawa kotu bayan hana shi sayen form da aka yi na tsayawa takarar shugabancin jam’iyar. Wani abu ne da zai iya haifar da babbar matsala a cikin jami’iyar a gaba.

Duk kuwa da cewar kotu ta bada umurnin kada a yi wannan taron, baya ga karar da Lamido ya shigar, wata kotu ta bada akasasin wannan hukunci, shi yasa wasu ‘yan jam’iyyar cigaba da gabatar da taron.

Barista Bala, yana kira da mahukunta da su dinga mutunta hukuncin kotu, da kuma yin amfani da matsayin su na siyasa don yin garon bawul ga bangaren shari’ar kasar, don gujewa irin wadannan matsalokin.

Yana kuma ganin wannan taron bashi da hurumin zaben wannan shugaban da suke ikirarin sun yi da kuma korar wasu ‘yan jam’iyar. Lallai babu shakka idan aka koma wajen wannan kotun zata soke wannan taron, da cire sabon shugaban jam’iyyar da aka zaba.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/Rikicin-Jamiyyar-PDP.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Zelensky Na Ukraine Zai Gana Da Takwaransa Na Faransa A Yau
Next Post: An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya!

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe Najeriya
NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas Najeriya
Margayi Shugaba Muhammadu Buhari 1942-2025 Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Barau Jibril: Mu Ba ‘Yan Amshin Shata Bane A Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Dogarawan Ruwa Na Amurka Suna Yunkurin Shiga Wani jirgin Dakon Mai Da Aka Allakan Ta Da Venezuela Labarai
  • Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist
    Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo Wasanni
  • Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
  • Gasar Cin Kofin Nahiyar Afrika A Wannan Makon Wasanni
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gaza Ga Albarusai Ga Yunwa Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.