Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Salmanu: Ci Gaban Wikki Tourist FC Shine A Gaba Na
Published: January 5, 2026 at 7:41 AM | By: Bala Hassan

Sabon Shugaban ƙungiyar Kwallon Kafa ta Wikki Tourist FC Bauchi dake tarayyar Najeriya Salmanu Abubakar yayi alkawarin kawo ci gaba a ƙungiyar.

Salmanu Abubakar ya ce tun kafin ya zo wannan matsayi dama ya san matsalolinta, domin ya rike matsayin Sakataren ƙungiyar magoya bayan Wikki.

Babban matsalar Wikki shine shishigi wajan shiga aikin da ba naka ba “in ji shi, a lokacin zantawarsu da wakilin GTA Hausa.

Saboda haka babban abunda ya farayi shine zama da ma’aikatan hukumar don gyara wannan lamari ta hanyar ko wa ya tsaya akan aikin sa, abunda bature ya ke ciwa (Division of labour) yin haka shine mataki gyara na farko wadda hakan zai kawo cigaba sosai.

Kan batun ‘yan wasa kuwa Salmanu yace ya dauki matakin gyara tun da dama rashin sanya kwallon a raga ita ce matsala to tuni ya gayyaci sabbin ‘yan wasa shida da zai’yi anfani da su a tsakiyar kakan wanan bana kuma kwaliya zata biya kudin sabulu wajan faranta wa magoya baya rai.

Ya kuma bada tabbacin zasu ba wa maihoras da ƙungiyar Abdullahi Maikaba, cikekken dama wajan gudanar da aikin sa don samun nasara wa ƙungiyar.

Salmanu yace kamar yadda maigirma Gwamnan jihar Bauchi Sanata Bala Abdulkadir Muhammad, ya basu amana don gyara da kuma kawo cigaba a wannan Ƙungiyar to bazasu ci amanan maigirma Gwamnan ba wajan aiki tukuru don samun nasara a wannan Ƙungiyar ta Wikki Tourist FC.

Da ya ke tsokaci ga me da ƙungiyar magoya bayan Wikki Tourist, Salmanu Abubakar ya ce wannan shine babban kalu balen sa amman akwai shiri da yakeyi don tabbacin adalci a duk bangarorin jihar Bauchi wajan sanya musu wakili a cikin wannan ƙungiya, bayan haka akwai wata horaswa ta musamman da za’a basu wajan yadda zasu gudanar da aikin yayin wasanni.

Daga karshe yayi alkawarin dawo da ƙungiyar cikin hayyacinta a teburin gasar Firimiyar lig na Najeriya ganin yadda kungiyar a yanzu ta ke wani matsayi da bai da ce ba.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Ana Jimamin Mutuwar Giwa Mai Shekaru Kusan 60 A Kasar Kenya
Next Post: Kauran Gwandu Zai Inganta Wutan Lantarki A Kebbi

Karin Labarai Masu Alaka

Kocin Ranchers Bees Ya Yi Murabus Wasanni
Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu Afrika
An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
Wasan Dambe Ya Dau Sabon Salo A Jihar Inugu Wasanni
Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Senegal Yaki Amincewa Da Hukuncin CFA Afrika
Barcelona na hangen Enrique Ko Arteta Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jagoran Kwankwasiya A Najeriya Ya Koma Jam’iyar ADC Labarai
  • Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace Labarai
  • Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
  • Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda Afrika
  • Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana Labarai
  • ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji Afrika
  • Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.