Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana
Published: January 8, 2026 at 1:16 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Dama dai tun a watan Junairun shekarar da ta gabata ne tsohon ministan kuɗaɗen Ghana, Ken Ofori-Atta ya tsere daga Accra zuwa Amurka da sunan neman lafiya.

Tsohon ministan wanda gwamnatin Accra ta zarge shi da badaƙalar maƙudan kuɗaɗe, har ma ta ce ya tsere daga ƙasar ne saboda gudun fuskantar shari’a, ya nemi tsawaita zamansa a Washington a cewar lauyoyinsa.

To amma jami’an hukumar shige da fice na ƙasar sun kama shi, inda zuwa yanzu babu masaniya game da inda aka ajiye shi a cikin Amurkan.

Sanarwar da tawagar lauyoyinsa suka fitar, ta ce suna tatttaunawa da jami’an tsaron Washington don ganin an sake shi nan bada jimawa ba, a cewarsu shi ma tsohon ministan yana bai wa jami’an haɗin kai.

Ofori-Atta, dai ya kasance ministan kuɗi na Ghana tun daga shekarar 2017 har zuwa ta 2024, zamanin mulkin tsohon shugaban ƙasar Nana Akufo-Addo, inda ya jagoranci aiwatar da sauye-sauye da dama a fannin tattalin arziƙin ƙasar, wanda gwamnatin John Dramani Mahama ke adawa da su.

Afrika, Amurka

Post navigation

Previous Post: Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara
Next Post: An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba.

Karin Labarai Masu Alaka

ECOWAS Ta Saka Dokar Ta Baci A Afrika Ta Yamma Afrika
Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
Farashin Mai Ya Doshi Dala 100 Kowacce Ganga Afrika
Gwamnatin Tarayya Za Ta Sake Fasalin Shirin NYSC Afrika
Tinubu Ya Jaddada Buƙatar Kare Rayukan ‘Yan Afirka A Taron ECOWAS Afrika
An Kai Shugaban Kasar Venezuela Kotu Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Gargadi Kasar Canada Game Da Tura Sojoji Lebanon Afrika
  • Najeriya Da Amurka Sun Amince Su Haɗa Kai Don Inganta ’Yancin Addini Da ƙarfafa Tsaro A Nijeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran: Za A Gudanar Da Jana’izar Khamenei Bayan Kwanaki Goma Na Muharram Afrika
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane Afrika
  • Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.