Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa
Published: November 20, 2025 at 3:25 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 20, 2025

Kungiyar Kwallon Kafa ta Enyimba dake ABA a Najeriya ta fidda wata takarda wacce ta raba wa manema labarai. Takardar dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na ƙungiyar SAMPSON ORJI.

Inda suke nisanta kansu da wani labari da ya ja hankali a shafin sada zumuntar zamani cewar ƙungiyar ta Enyimba FC. Ta rage Albashin ‘Yan Wasa da kashi 50% bayan shan kaye a gida a hannun Wikki Tourist FC. daci 1-0 cikin gasar firimiya lig na Najeriya mako na 13.

Kungiyar Enyimba FC tace babu wani lokaci da shugabanninta suka amince, suka fara, ko aiwatar da wani rage albashi, na yan wasanta ba.

“Wannan rahoton wani abu ne kawai na tunanin marubucin kuma ya kamata jama’a su yi watsi da shi.” inji Enyimba.

Kungiyar ta nuna damuwa cewa irin wannan labarin karya ya fito ne daga wata kafar yada labarai da ake kyautata zaton ba tare da wani yunkurin tabbatar da sahihanci daga kungiyar ko ta hanyar shugabanninta ko kafofin watsa labaranta ba.

Kungiyar Enyimba FC, na goyon bayan girmama juna da kafofin watsa labarai da suka dade suna yi, ta ci gaba da mayar da hankali kan komawa ga hanyoyin nasara.

“Za mu ci gaba da yin aiki kafada da kafada da abokan hulɗar kafofin watsa labarai, don haskaka ayyukanmu da kuma ba da gudummawa ga ci gaban NPFL da ci gaban ƙwallon ƙafa a Najeriya.”

Hukumar shirya gasar cin kofin (NNL) a Najeriya ta tabbatar da janyewar ƙungiyar kwallon kafa ta Dakkada FC da ke Uyo daga gasar NNL26 mai zuwa.

“Hukumar ta yi alƙawarin daidaita jadawalin wasannin domin samar da hanyoyin da za a bi wajen cimma burin da aka sa a gaba. Hakan ya zama dole saboda janyewar ƙungiyar DAKKADA FC daga gasar.” Inji Hukumar.

DAGA KASAR GHANA:

Wani mamba a hukumar kula da wasan kwallon kafa ta kasar Ghana (GFA) Frederick Acheampong, ya ziyarci magoya bayan kulub din Aduana FC da suka ji rauni a wani hatsari a kan hanyarsu ta dawowa gida, bayan wasan GPL da su kayi da ƙungiyar kwallon kafar Asante Kotoko a Kumasi.

Hatsarin da ya jawo harda rasa rayuka. Frederick ya mika ta’aziyya ga iyalai da duk masoyan magoya bayan biyu da suka rasa rayukansu a hatsarin.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/RAHOTON-WASANNI-DARE-19-11-2025.mp3
Wasanni

Post navigation

Previous Post: An Gudanar Da Taron Matasan Kasashe 6, Don Kawo Karshen Ta’addanci
Next Post: Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz

Karin Labarai Masu Alaka

Najeriya Na ƙoƙarin Shiga Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Ta Barauniyar Hanya Wasanni
CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni
Yan Fashi Sun Shiga Gidan Alex Iwobi A Ingila Wasanni
Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot. Wasanni
Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Jihar Yobe: Ana Cin Zarafin Fursunoni A Gidan Gyaran Halin Potiskum Tsaro
  • Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Umar Ya Lashe Kyautar Gwarzon ‘Dan-Wasa Na 2025 Wasanni
  • An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi Labarai
  • Bassirou: Tawagar Senegal Zasu Samu Kyautar Kudi Da Filaye Sakamakon Nasarar Da sukayi AFCON 2025 Wasanni
  • Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya Afrika
  • Iran Zata Shigar Da Lebanon Cikin Cimma Yarjejeniya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.