Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci Afrika
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika
  • Jihar Gombe Ta Karbi Bakuncin Taron Tsaro Tsakanin DIG Da Masu Ruwa Da Tsaki Afrika
  • Sauya Sunan Lafarge Africa Zuwa HBM Nigeria Plc Zai Samar Da Cigaba – Sarkin Fulanin Gombe Afrika

Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa
Published: November 20, 2025 at 3:25 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 20, 2025

Kungiyar Kwallon Kafa ta Enyimba dake ABA a Najeriya ta fidda wata takarda wacce ta raba wa manema labarai. Takardar dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na ƙungiyar SAMPSON ORJI.

Inda suke nisanta kansu da wani labari da ya ja hankali a shafin sada zumuntar zamani cewar ƙungiyar ta Enyimba FC. Ta rage Albashin ‘Yan Wasa da kashi 50% bayan shan kaye a gida a hannun Wikki Tourist FC. daci 1-0 cikin gasar firimiya lig na Najeriya mako na 13.

Kungiyar Enyimba FC tace babu wani lokaci da shugabanninta suka amince, suka fara, ko aiwatar da wani rage albashi, na yan wasanta ba.

“Wannan rahoton wani abu ne kawai na tunanin marubucin kuma ya kamata jama’a su yi watsi da shi.” inji Enyimba.

Kungiyar ta nuna damuwa cewa irin wannan labarin karya ya fito ne daga wata kafar yada labarai da ake kyautata zaton ba tare da wani yunkurin tabbatar da sahihanci daga kungiyar ko ta hanyar shugabanninta ko kafofin watsa labaranta ba.

Kungiyar Enyimba FC, na goyon bayan girmama juna da kafofin watsa labarai da suka dade suna yi, ta ci gaba da mayar da hankali kan komawa ga hanyoyin nasara.

“Za mu ci gaba da yin aiki kafada da kafada da abokan hulɗar kafofin watsa labarai, don haskaka ayyukanmu da kuma ba da gudummawa ga ci gaban NPFL da ci gaban ƙwallon ƙafa a Najeriya.”

Hukumar shirya gasar cin kofin (NNL) a Najeriya ta tabbatar da janyewar ƙungiyar kwallon kafa ta Dakkada FC da ke Uyo daga gasar NNL26 mai zuwa.

“Hukumar ta yi alƙawarin daidaita jadawalin wasannin domin samar da hanyoyin da za a bi wajen cimma burin da aka sa a gaba. Hakan ya zama dole saboda janyewar ƙungiyar DAKKADA FC daga gasar.” Inji Hukumar.

DAGA KASAR GHANA:

Wani mamba a hukumar kula da wasan kwallon kafa ta kasar Ghana (GFA) Frederick Acheampong, ya ziyarci magoya bayan kulub din Aduana FC da suka ji rauni a wani hatsari a kan hanyarsu ta dawowa gida, bayan wasan GPL da su kayi da ƙungiyar kwallon kafar Asante Kotoko a Kumasi.

Hatsarin da ya jawo harda rasa rayuka. Frederick ya mika ta’aziyya ga iyalai da duk masoyan magoya bayan biyu da suka rasa rayukansu a hatsarin.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/RAHOTON-WASANNI-DARE-19-11-2025.mp3
Wasanni

Post navigation

Previous Post: An Gudanar Da Taron Matasan Kasashe 6, Don Kawo Karshen Ta’addanci
Next Post: Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz

Karin Labarai Masu Alaka

Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni
Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo Wasanni
An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
Bana Ba Harka Ga ‘Yan-Wasan Kwallon Kafar Najeriya Wasanni
Wikki Tourists FC: Ta Yi Sabbin ‘Yan Wasa Uku Wasanni
CAF Ta Ci Tarar Ƙasar Masar Dala 5,000 AFCON 2025 Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa
  • Dan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar APM A Bauchi Ya Bada Gudummawar Naira Miliyan ₦21 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Bara Da Shira
  • Idan Allah Yasa Muka Kafa Gwamnati Zamu Kyautata Wa Ma’aikata Yakubu Adamu Dan Takarar Kujeran Gwamnan Bauchi
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Da Iran Sun Tattauna A Kasar Pakistan Afrika
  • Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Rasha: Tura Sojojin Birtaniya Ukraine Zai Kara Ta’azzara Yaki Labarai
  • Sakamakon Rikicin Gabas Ta Tsakiya Farashin Mai Ya Karu Labarai
  • Ambaliyar Ruwa Ya Tilastawa Dubban Jama’a Rasa Muhallensu A Morocco Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.