Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano!
Published: November 20, 2025 at 5:13 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Masana da manazarta a fannin tattalin arziki a Najeriya sun fara fashin baki akan kasafin kudi da Gwamnatin jihar Kano ta shirya domin tunkarar shekarar kudi ta badi.

A jiya Laraba ne dai gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gabatar da kasafin a zauren majalisar dokokin, inda yace gwamnatin jihar ta shirya kashe kusan naira triliyon guda da rabi a shekarar kudi ta 2026 dake tafe.

Yace bangaren ilimin shine ya samu kaso mafi tsoka da kashi 30 cikin dari, yayin da aka kebewa fannin ayyukan raya kasa kashi 68 na gundari kasafin, inda gwamnati zata maida hankali akan kammala ayyaka da ake gudanarwa tare da kirkiro wasu sabbi.

Sai dai masanin tattalin arziki, Dr. Abdussalam Kani, yace alkaluman dake cikin kasafin sun ci karo da alkaluman da aka fitar a yayin taro na masu ruwa da tsaki, da kwararru kan tattalin arziki da Jami’an gwamnatin Kano da akayi a kwanakin baya, game da hasashen abin da gwamnatin ka iya samu na kudaden shiga a badi.

Yace yanzu kalubale ne akan majalisar dokokin ta Kano ta dai-daita alkaluman kasafin na kusan Naira tiriliyon guda da rabi, domin kuwa sun zarce alkaluman da ke cikin takardar M-TEF, wadda aka mikawa majalisar dokokin gabanin gwamnan ya gabatar da kasafin.

Dr Abdussalam Kani yace takardar M-TEF, mai dauke da hasashen da masana da Jami’an gwamnati game da kudaden shiga na gwamnati a shekara ta 2026 wadda bai wuce naira biliyan dari takwas ba, kuma doka tace tilas ne kasafin da gwamna ya shirya yayi dai-dai da hasashen masana cikin takardar M-TEF.

A nasa bangaren, comrade Salisu Gambo, gudana cikin ‘yan gwagwarmayar shugabanci na gari a Najeriya, yace kamata yayi ace banaren tsaro na biye da na ilimi wajen samun kaso mafi tsoka a cikin kasafi, a don haka akwai bukatar majalisar dokokin ta sake nazarin kason da aka kebewa al’amuran tsaro a jihar.

A nan gaba ne, ake sa ran majalisar dokokin zata kira taron jin ra’ayin jama’a, domin karbar kasidu da shawarwari daga kungiyoyi da dedekun mutane kan yadda suke ganin za’a inganta kasafin domin ya dace da muhimman bukatun al’umar jihar ta Kano su fiye da miliyan 20.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/Kasafin-Kudin-Jihar-Kano-2026.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz
Next Post: Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Bola Tinubu Ya Tafi Turai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna Najeriya
An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
Matatar Man Dangote Ta Samu Tagomashi Daga Abokan Hulda Najeriya
Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki Najeriya
Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • NAHCON Tafara Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2026 Najeriya
  • Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
  • Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mataimakin Gwamnan Bayelsa Najeriya
  • Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wani Ya Yiwa ‘Yar Sa Mai Shekaru 8 Fyade A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
  • An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.