Kotu a kasar Uganda ta bada belin wata ‘yar gwagwarmaya me rajin kare hakki da ake karin tsare ta matsayin wani yunkuri na durkusar da duk wani dan adawa kafin zaben shugaban kasa da aka gudanar ranar 15 ga wannan watan.
An tsare Sarah Bireete ne tun ranar 30 ga Watan Disambar bara, bayan da ta kalubalanci ingancin registar zabe da za’a yi amfani da ita wajen kada kuri’a. Daga baya aka tuhume ta da bayyana bayanai kan masu zabe ta hanyar da ta sabawa doka.
Sarah Bireete ita ce shugabar wata kungiya mai neman aiwatar da tsarin mulki bisa doka, a Kampala.
A yau ne alkalin magitire Nankya Jatico ta bada belin ta, tana me cewa ta cika duk wasu sharuda da suka cancanta a bata beli.


