Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita
Published: November 22, 2025 at 3:30 AM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 23, 2025

Masana harkokin tsaro a Najeriya sun bayyana cewa kyakkyawar alaka da fahinta tsakanin jami’an tsaro da al’umma, suna da gagarumin tasiri wajen magance matsalolin tsaro da samun zaman lafiya mai dorewa.
A wata tattaunawa ta musamman da sashen hulda tsakanin farar hula da jami’an soji da shelkwatar rundunar ta shirya da manema labarai a Jos, jihar Filato, masana harkokin tsaro, jami’an soji da ‘yan jarida sun dauki wuni guda suna fadakar da juna matakan da kowa zai bi wajen samadda masalaha kan matsalolin tsaro da suka addabi Najeriya.
Birgediya Janar Sani Usman Kukasheka mai ritaya, wanda ya gabatar da kasida mai taken “Tasirin Fasahar dake tasowa kan kafafen watsa labarai da hadin gwiwa tsakanin soji da kafafen watsa labarai”, ya bayyana cewa idan har ‘yan jarida sun fahinci yadda soja ke gudanar da aikinsu, suka kuma fadakar da al’umma, ba shakka za’a sami ci gaba.
Madam Ayuku Pwaspo, shugabar kungiyar ‘yan Jarida ta kasa reshen jihar Filato, ta bukaci manema labarai su gudanar da aikinsu bisa ka’ida don hadin kan kasa.
Shugaban sashen hulda tsakanin farar hula da soji, Manjo Janar Musa Etsu-Ndagi yace ‘yan jarida na da gagarumin gudunmawar fadakar da jama’a yadda soja ke aiki.
Hajiya Hadiza Hassan, ‘yar jarida dake aiki a gidan Rediyo da Talabijin na Unity a Jos, tace ta karu sosai daga tattaunawar.
Wassu faifan bidiyo da hotuna da rundunar sojin da nuna sun bayyana irin tallafi da sojoji ke baiwa al’umma da suka hada da gyara da gina makarantu da asibitoci, tallafin kayan abinci ga wadanda suka shiga ibtila’i da sauransu.
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Manya-Manyan Wasannin Wannan Makon
Next Post: Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno Afrika
Mayakan Boko Haram Da ISWAP Sun Kai Hari Cikin Dare Afrika
Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika
Man Da Matatar Dangote Take Fitarwa Zuwa Kasashen Afirka Ya Karu Afrika
Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai
An Kusa Kawo Karshen Matsalolin Tsaro A Jihar Filato Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
  • Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Da Tarayyar Turai Sun Fidda Sanarwa Afrika
  • Tsohon Lauyan Amurka Jack Smith Ya Fadi Maganganu Game Da Donald Trump Amurka
  • “Yan Wasan Super Eagles Sun Karbi Alkawarin Da Gwamnati Tayi Musu AFCON 2023 Labarai
  • Baitul Malin Amurka Zata Bawa Venezuela Da Cuba Damar Sayar Da Mai Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.