Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia
Published: February 10, 2026 at 11:32 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Dubban mutane ne suka yi zanga zanga fadin kasar Australia ranar Litinin, domin nuna adawa da fara ziyarar da shugaban jeka nayika na Isra’ila Isaac Herzog yake yi a wasu biranen kasar, domin karfafa dangantaka da jajantawa yahudawan dake kasar bayan mummunar harin da aka kai musu a bara.

Herzogg ya kai ziyara Australia cikin makon nan, bayan da PM kasar Anthony Albanese ya gayyace shi bayan harin da aka kai kan taron yahudawa da suke bikin addinin su a gabar ruwan kasar ranar 14 ga watan Disamba bara, har maharan suka kashe mutane 15.

Ziyarar da shugaba Herzogg yake yi ta harzuka wasu mutane a kasar wadanda suke zarginsa cewa yana da hanu a kashe farar hula a Gaza. Kungiyoyi da suke goyon bayan Falasdinawa sun shirya zanga zanga a birane da garuruwa a duk kasar a yammacin ranar Litinin.

Dubban mutane ne suka hallara a wani dandali a birnin Sydney suna sauraron jawabai suna ambaton kalaman goyon baya ga Falasdinawa.

Afrika, Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata
Next Post: Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado

Karin Labarai Masu Alaka

Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar Labarai
Trump Da Bin Salman Da Wasu Kasashe Za Su Sa Hannu A Rikicin Sudan Labarai
Wani Alkali A Kotun Amurka Ya Dakatar Da Kudurin Shugaba Trump Afrika
Masar Tayi Yarjejeniyar Makamashi Da Kasashen Norway Da China Labarai
Kasar Netherland Ta Mayarwa Masar Mutum Mutumin Tarihi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kwankwaso: Gwamnatin Kano Tamuce Baki Daya, Tafiya APC Allah Ya Raka Taki Gona! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Pakistan Zata Karbi Bakwancin Saudiya, Turkiyya Da Masar Afrika
  • Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran Afrika
  • Ganduje: Mun Janye Shirin Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano Najeriya
  • Tawagar Shirya Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Ta Ziyarci Masarautun Jihar Labarai
  • Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
  • FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya Najeriya
  • Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.