Mutum biyu sun mutu a wani rikici yayin zaɓen shugabannin APC a Ondo
Rundunar ‘yan sanda ta jihar Ondo ta tabbatar da mutuwar mutum biyu tare da jikkata wasu uku sakamakon rikicin da ya ɓarke a taron zaɓen shugabannin mazabu na jam’iyyar APC a Idanre.
Mai magana da yawun rundunar, Abayomi Jimoh, ya ce lamarin ya faru ne a ranar 18 ga Faburairu da misalin ƙarfe 11:05 na safe bayan samun kiran gaggawa daga DPO na yankin.
Ya bayyana cewa Kwamishinan ‘yan sanda, Adebowale Lawal, ya tura rundunonin musamman tare da haɗin gwiwar jami’an Civil Defense domin daƙile rikicin da dawo da zaman lafiya.
Rahotanni sun nuna cewa an kai hari ga mutane biyar tare da banka wa mota wuta, inda uku daga cikin waɗanda aka kai wa harin na karɓar magani, yayin da aka tabbatar da mutuwar biyu a asibiti.

‘Yan sanda sunce ana ci gaba da bincike domin gano waɗanda suka aikata laifin, tare da ɗaukar matakan tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a jihar.


