Rahotanni daga hukumomin tsaro a Kenya sunce fiye da ‘yan kasar dubu daya ne aka dauka domin yaki da dakarun Rasha a Ukraine, kamar yadda bayanai da hukumomin tsaron kasar suka gabatarwa wakilan majalisar dokokin kasar a makon nan, wannan adadi ya ninka sau biyar kan kiyasin farko da hukumomin kasar suka yi.
Sai dai ofishin jakadancin Rasha a Nairobi ranar Alhamis ta musanta cewa Rasha tana da hanu wajen daukar ‘yan kasar Kenya ba bisa ka’ida ba domin su taimake ta da yaki a Ukraine, amma tace ‘yan kasashen ketare domin radin kansu suna iya shiga rundunar sojan kasar.
Da yake karanta rahoton ga wakilan majalisar, shugaban masu rinjaye a majalisar dokokin kasar, ya zargi wasu baragurbin ma’aikatan gwamnati da suke hada baki da miyagun kungiyoyi masu safrar mutane wajen daukar ‘yan kasar kenya domin shiga yaki a ukraine a amadadin Rasha.
Masu daukar su aikin suna auna tsoffin sojoji da ‘Yan sanda, da kuma marasa ayyukan yi, tare da yi musu alkawarin za a biya su dala dubu biyu da dari bakwai da 15 a ko wani wata sannan za’a ba su dala dubu tara da dari uku da tara a zaman tukuici.
Zuwa wannan wata na Faburairun , yanzu haka akwai ‘yan kasar Kenya 89 a fagen daga a Ukraine, 39 suna asibiti, yayinda wasu 28 sun bace a fagen yaki ba’a sn inda suke ba.


