Gwamnan jihar Adamawa, Umaru Fintiri, ya sanar da komawarsa jam’iyyar All Progressives Congress (APC), matakin da ya ƙara wa jam’iyyar ta Bola Ahmed Tinubu ƙarfi da tasiri a jihar.
Gwamnan ya bayyana hakan ne cikin wani jawabi da ya gabatar a ranar Juma’a, inda ya ce ya ɗauki wannan mataki ne bisa la’akari da muradun ci gaban al’ummar jihar Adamawa.
Fintiri ya kuma bayyana cewa bai sauya sheƙa shi kaɗai ba, domin ya tafi tare da mambobin majalisar zartaswa ta jiha, ’yan majalisar dokoki da sauran manyan jami’an jam’iyyar People’s Democratic Party (PDP) a jihar. Wannan lamari ya ƙara wa APC rinjaye a fagen siyasar Adamawa.
Tasirin Lamarin ga Atiku
Masu nazarin harkokin siyasa na ganin cewa wannan sauyi na iya zama babban ƙalubale ga tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, wanda shi ma ɗan asalin Jihar Adamawa ne.
Sauyin na zuwa ne gabanin babban zaɓen shugaban ƙasa mai zuwa, kuma ana ganin zai iya sauya ma’aunin siyasa a jihar, wadda ake kallonta a matsayin muhimmin sansani a arewacin ƙasar.
Har zuwa yanzu dai ba a fitar da wata sanarwa daga Atiku kan wannan mataki ba.


